ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Rabon Tirelolin Taki 135 A Zamfara

by Leadership Hausa and Sulaiman
1 year ago
Dauda

A wani gagarumin yunƙuri na bunƙasa ayyukan noma, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ƙaddamar da rabon tireloli 135 na takin zamani ga manoma a faɗin ƙananan hukumomin jihar 14.

 

An ƙaddamar da rabon takin ne a ranar Talata a Ma’aikatar Noma ta jihar Zamfara, inda aka ajiye takin.

ADVERTISEMENT
  • Mutane 4 Sun Mutu, 6 Sun Bace Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Kano
  • Za A Gudanar Da Bikin CIFTIS Na Shekarar 2024 A Birnin Beijing

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce, za a raba buhunan taki iri-iri 81,000 kyauta ga manoma 40,500 a faɗin ƙananan hukumomi 14 na Jihar Zamfara.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

Sanarwar ta ƙara da cewa, a wajen ƙaddamar da shirin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na haɓaka noma a Zamfara ta hanyar taimakawa manoma wajen bunƙasa noman su. “Za mu ci gaba da ƙoƙarinmu don magance ƙalubale a fannin noma.”

 

Gwamnan ya ce, “Mun ƙuduri aniyar tunkarar ƙalubale da kuma bai wa manoman mu goyon baya da ƙarfafa musu gwiwa don tabbatar da ci gaban al’umma da tattalin arzikin jihar.

 

“A ’yan watannin da suka gabata na ziyarci ɗaukacin ƙananan hukumomi 14 domin ƙaddamar da rabon takin zamani da sauran kayayyakin noma ga manoman mu a ƙarƙashin shirin NG-CARES. Taki wani muhimmin abu ne na samar da amfanin gona yayin da yake haɓaka samar da abinci, yana ƙara yawan amfanin gona, da haɓaka ingancin kayan amfanin gona.

 

“Za mu ci gaba da yin aiki tuƙuru domin tabbatar da cewa noman bai taƙaita da damina kaɗai ba, ya zama abu ne da ake yi a duk faɗin shekarar wanda manoman mu za su kasance cikin aiki a koda yaushe. Ta yin haka, za mu iya cimma burinmu na samun ikon mallakar abinci da kuma ƙara samun kuɗin shiga na manoma.

 

“Kafin in kammala, ina kira ga waɗanda suka amfana da wannan karimcin da su yi amfani da waɗannan takin yadda ya kamata. Ina kuma ƙara tabbatar muku da irin goyon bayan da muke bayarwa wajen samar da yanayi mai kyau ga noman noma a faɗin jihar nan domin bai wa manoman mu damar komawa gonakinsu ba tare da wata fargaba ba.

 

“Da waɗannan kalamai, abin alfaharina ne na ƙaddamar da rabon tireloli 135 na taki iri-iri ga manoma a faɗin ƙananan hukumomin jiharmu 14 domin noman damina a jihar Zamfara a shekarar 2024.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN
Manyan Labarai

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Next Post
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai Na Sin Da Afirka Karo Na 6

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai Na Sin Da Afirka Karo Na 6

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.