• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Rabon Tirelolin Taki 135 A Zamfara

by Leadership Hausa and Sulaiman
1 year ago
Dauda

A wani gagarumin yunƙuri na bunƙasa ayyukan noma, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ƙaddamar da rabon tireloli 135 na takin zamani ga manoma a faɗin ƙananan hukumomin jihar 14.

 

An ƙaddamar da rabon takin ne a ranar Talata a Ma’aikatar Noma ta jihar Zamfara, inda aka ajiye takin.

  • Mutane 4 Sun Mutu, 6 Sun Bace Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Kano
  • Za A Gudanar Da Bikin CIFTIS Na Shekarar 2024 A Birnin Beijing

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce, za a raba buhunan taki iri-iri 81,000 kyauta ga manoma 40,500 a faɗin ƙananan hukumomi 14 na Jihar Zamfara.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

Sanarwar ta ƙara da cewa, a wajen ƙaddamar da shirin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na haɓaka noma a Zamfara ta hanyar taimakawa manoma wajen bunƙasa noman su. “Za mu ci gaba da ƙoƙarinmu don magance ƙalubale a fannin noma.”

 

Gwamnan ya ce, “Mun ƙuduri aniyar tunkarar ƙalubale da kuma bai wa manoman mu goyon baya da ƙarfafa musu gwiwa don tabbatar da ci gaban al’umma da tattalin arzikin jihar.

 

“A ’yan watannin da suka gabata na ziyarci ɗaukacin ƙananan hukumomi 14 domin ƙaddamar da rabon takin zamani da sauran kayayyakin noma ga manoman mu a ƙarƙashin shirin NG-CARES. Taki wani muhimmin abu ne na samar da amfanin gona yayin da yake haɓaka samar da abinci, yana ƙara yawan amfanin gona, da haɓaka ingancin kayan amfanin gona.

 

“Za mu ci gaba da yin aiki tuƙuru domin tabbatar da cewa noman bai taƙaita da damina kaɗai ba, ya zama abu ne da ake yi a duk faɗin shekarar wanda manoman mu za su kasance cikin aiki a koda yaushe. Ta yin haka, za mu iya cimma burinmu na samun ikon mallakar abinci da kuma ƙara samun kuɗin shiga na manoma.

 

“Kafin in kammala, ina kira ga waɗanda suka amfana da wannan karimcin da su yi amfani da waɗannan takin yadda ya kamata. Ina kuma ƙara tabbatar muku da irin goyon bayan da muke bayarwa wajen samar da yanayi mai kyau ga noman noma a faɗin jihar nan domin bai wa manoman mu damar komawa gonakinsu ba tare da wata fargaba ba.

 

“Da waɗannan kalamai, abin alfaharina ne na ƙaddamar da rabon tireloli 135 na taki iri-iri ga manoma a faɗin ƙananan hukumomin jiharmu 14 domin noman damina a jihar Zamfara a shekarar 2024.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Next Post
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai Na Sin Da Afirka Karo Na 6

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai Na Sin Da Afirka Karo Na 6

LABARAI MASU NASABA

Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

October 15, 2025
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.