ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Rabon Tirelolin Taki 135 A Zamfara

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Dauda

A wani gagarumin yunƙuri na bunƙasa ayyukan noma, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ƙaddamar da rabon tireloli 135 na takin zamani ga manoma a faɗin ƙananan hukumomin jihar 14.

 

An ƙaddamar da rabon takin ne a ranar Talata a Ma’aikatar Noma ta jihar Zamfara, inda aka ajiye takin.

ADVERTISEMENT
  • Mutane 4 Sun Mutu, 6 Sun Bace Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Kano
  • Za A Gudanar Da Bikin CIFTIS Na Shekarar 2024 A Birnin Beijing

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce, za a raba buhunan taki iri-iri 81,000 kyauta ga manoma 40,500 a faɗin ƙananan hukumomi 14 na Jihar Zamfara.

 

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Sanarwar ta ƙara da cewa, a wajen ƙaddamar da shirin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na haɓaka noma a Zamfara ta hanyar taimakawa manoma wajen bunƙasa noman su. “Za mu ci gaba da ƙoƙarinmu don magance ƙalubale a fannin noma.”

 

Gwamnan ya ce, “Mun ƙuduri aniyar tunkarar ƙalubale da kuma bai wa manoman mu goyon baya da ƙarfafa musu gwiwa don tabbatar da ci gaban al’umma da tattalin arzikin jihar.

 

“A ’yan watannin da suka gabata na ziyarci ɗaukacin ƙananan hukumomi 14 domin ƙaddamar da rabon takin zamani da sauran kayayyakin noma ga manoman mu a ƙarƙashin shirin NG-CARES. Taki wani muhimmin abu ne na samar da amfanin gona yayin da yake haɓaka samar da abinci, yana ƙara yawan amfanin gona, da haɓaka ingancin kayan amfanin gona.

 

“Za mu ci gaba da yin aiki tuƙuru domin tabbatar da cewa noman bai taƙaita da damina kaɗai ba, ya zama abu ne da ake yi a duk faɗin shekarar wanda manoman mu za su kasance cikin aiki a koda yaushe. Ta yin haka, za mu iya cimma burinmu na samun ikon mallakar abinci da kuma ƙara samun kuɗin shiga na manoma.

 

“Kafin in kammala, ina kira ga waɗanda suka amfana da wannan karimcin da su yi amfani da waɗannan takin yadda ya kamata. Ina kuma ƙara tabbatar muku da irin goyon bayan da muke bayarwa wajen samar da yanayi mai kyau ga noman noma a faɗin jihar nan domin bai wa manoman mu damar komawa gonakinsu ba tare da wata fargaba ba.

 

“Da waɗannan kalamai, abin alfaharina ne na ƙaddamar da rabon tireloli 135 na taki iri-iri ga manoma a faɗin ƙananan hukumomin jiharmu 14 domin noman damina a jihar Zamfara a shekarar 2024.”

Dauda
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Dauda
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai Na Sin Da Afirka Karo Na 6

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai Na Sin Da Afirka Karo Na 6

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.