ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Rabon Tirelolin Taki 135 A Zamfara

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Dauda

A wani gagarumin yunƙuri na bunƙasa ayyukan noma, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ƙaddamar da rabon tireloli 135 na takin zamani ga manoma a faɗin ƙananan hukumomin jihar 14.

 

An ƙaddamar da rabon takin ne a ranar Talata a Ma’aikatar Noma ta jihar Zamfara, inda aka ajiye takin.

ADVERTISEMENT
  • Mutane 4 Sun Mutu, 6 Sun Bace Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Kano
  • Za A Gudanar Da Bikin CIFTIS Na Shekarar 2024 A Birnin Beijing

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce, za a raba buhunan taki iri-iri 81,000 kyauta ga manoma 40,500 a faɗin ƙananan hukumomi 14 na Jihar Zamfara.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Sanarwar ta ƙara da cewa, a wajen ƙaddamar da shirin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na haɓaka noma a Zamfara ta hanyar taimakawa manoma wajen bunƙasa noman su. “Za mu ci gaba da ƙoƙarinmu don magance ƙalubale a fannin noma.”

 

Gwamnan ya ce, “Mun ƙuduri aniyar tunkarar ƙalubale da kuma bai wa manoman mu goyon baya da ƙarfafa musu gwiwa don tabbatar da ci gaban al’umma da tattalin arzikin jihar.

 

“A ’yan watannin da suka gabata na ziyarci ɗaukacin ƙananan hukumomi 14 domin ƙaddamar da rabon takin zamani da sauran kayayyakin noma ga manoman mu a ƙarƙashin shirin NG-CARES. Taki wani muhimmin abu ne na samar da amfanin gona yayin da yake haɓaka samar da abinci, yana ƙara yawan amfanin gona, da haɓaka ingancin kayan amfanin gona.

 

“Za mu ci gaba da yin aiki tuƙuru domin tabbatar da cewa noman bai taƙaita da damina kaɗai ba, ya zama abu ne da ake yi a duk faɗin shekarar wanda manoman mu za su kasance cikin aiki a koda yaushe. Ta yin haka, za mu iya cimma burinmu na samun ikon mallakar abinci da kuma ƙara samun kuɗin shiga na manoma.

 

“Kafin in kammala, ina kira ga waɗanda suka amfana da wannan karimcin da su yi amfani da waɗannan takin yadda ya kamata. Ina kuma ƙara tabbatar muku da irin goyon bayan da muke bayarwa wajen samar da yanayi mai kyau ga noman noma a faɗin jihar nan domin bai wa manoman mu damar komawa gonakinsu ba tare da wata fargaba ba.

 

“Da waɗannan kalamai, abin alfaharina ne na ƙaddamar da rabon tireloli 135 na taki iri-iri ga manoma a faɗin ƙananan hukumomin jiharmu 14 domin noman damina a jihar Zamfara a shekarar 2024.”

Dauda
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
Dauda
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • Sulaiman
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

MASU ALAKA

Dauda
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa
Manyan Labarai

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Next Post
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai Na Sin Da Afirka Karo Na 6

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai Na Sin Da Afirka Karo Na 6

LABARAI MASU NASABA

Dauda

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Dauda

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Dauda

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.