• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Ya ‘Yantar Da Wasu Ɗaurarru 31 Da Ke Zaman Waƙafi A Gidan Yarin Gusau

by Leadership Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Gwamna Dauda Ya ‘Yantar Da Wasu Ɗaurarru 31 Da Ke Zaman Waƙafi A Gidan Yarin Gusau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A  ranar Juma’a ne gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya kai ziyara gidan gyara hali da ke Gusau, inda ya sanya aka saki ɗaurarru 31, kamar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya ya ba shi dama.

 

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa, gwamnan Dauda ya yanke shawarar yin haka ne bisa natsattsen binciken da aka gudanar game da waɗannan masu zaman wakafin.

  • Kungiyar Masu Masana’antu Sun Yi Hasashen Matsala Ga Sashen
  • Babban Layin Samar Da Wutar Lantarkin Nijeriya Ya Lalace Sau 7 A 2024

Sanarwar ta ƙara da cewa, tsarin mulki ya ba gwamnoni damar sassauta zaman yari ko ma yafiya ga wadanda ke zaman gidan yari.

 

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Cikin jawabin da ya gabatar a wurin sanya hannu a wannan yafiya, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, ɗaurarru ne masu laifuka daban-daban aka yafe musu domin a ƙarfafa musu gwiwa su zama ‘yan ƙasa nagari masu bin doka da oda.

Gwamna Dauda

“A yau na aiwatar da ikon da kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999, sashe na 212(1) ya ba ni, wanda ke da nufin yaye duk wani ƙunci da damuwa ga masu zaman gidan yari.

“An yanke wannan shawara ne bayan zurfafa binciken da aka yi game da waɗannan ɗaurarru, wanda kuma ya tabbatar da da-na-saninsu bisa abinda suka aikata a baya.

 

“Bugu da ƙari, na amince a bai wa kowanne daga cikinsu Naira 50,000 don su samu abin dogaro da kai bayan fitar su cikin jama’a.

 

“Wannan yana daga cikin ƙoƙarin gwamnati na na rage cunkoso a gidajen yari, musamman a wannan lokacin da muke yawan kamo ‘yan bindiga da masu ba su bayanan sirri.” In ji Gwamna Dauda

 

Bayan zagaya cikin gidan yarin, Gwamna Lawal ya yi alƙawarin bayar da taimakon da ya wajaba ga gidan yarin da ke Gusau.

Gwamna Dauda

Tun farko a nasa jawabin, shugaban Hukumar kula da gidajen gyaran hali ta jihar Zamfara, Dr. Umar Galadima, ya jinjina wa Gwamna Lawal bisa ziyarar da ya kai, tare da yafe wa ɗaurarrun.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gidan Gyara HaliTa'addancin 'yan bindiga a Zamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kudin Hadaka Na Fansho Ya Kai Naira Tiriliyan 21 A Watan Agusta

Next Post

Wakilin MƊD Ya Nuna Alhini Kan Fashewar Tankar Mai A Jigawa

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

2 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

2 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

4 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

4 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

6 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

7 hours ago
Next Post
Wakilin MƊD Ya Nuna Alhini Kan Fashewar Tankar Mai A Jigawa

Wakilin MƊD Ya Nuna Alhini Kan Fashewar Tankar Mai A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.