ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Masu Masana’antu Sun Yi Hasashen Matsala Ga Sashen

by Bello Hamza
2 years ago
Kungiyar

Darakta Janar ba kungiyar masana’antu na kasa MAN Segun Ajayi-Kadir, ya nuna damuwarsa a kan yadda a zango na hudu na 2024 matsin tattalin arzikin kasar, ke ci gaba da zamowa masu gudanar da masana’antu a kasar, gazaya tsayawa a kan kafafunsu.

Segun, a hirarsa da jaridar The PUNCH ya danganta hauhawan farashin kayan da suke gudanar da ayyukansu, wanda jakan ke janyo masu raguwar kayan da suke sarrafawa.

  • Wadanne Sakamako Aka Samu Daga Cinikin Tsakanin Sin Da Kasashen Ketare
  • An Kashe Mutane 5 A Wani Sabon Hari A Filato

Kazalika, ya danganta hauhawan kudin ruwa na bankuna, da tsadar man Dizil da karin farashin kudin wutar lantaki, a matsayin manyan da ke ci gaba da zamowa fannin babban kalubale duk da cewa masana’antun kasar, sun samar da gudaunmawar kashi 8.46 ga tattalin arzkin kasar a zango na biyu na 2024.

ADVERTISEMENT

Sai dai, gudunmawar da masana’antun kasar suka samar ga tattalin arzkin kasar, ta ragu daga kashi 8.62 a zango na biyu na 2023, inda raguwar ta fi kamari a zango na daya na 2024, wadda ta kai kashi 9.98.

Hakazalika, a cikin rahoton kundin da ‘ya’yan kungiyar suka tattara a zango na rabin shekarar 2024, sun koka a kan kaluabalen samun karin kudin ruwa na bankuna.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

A watan Satumbar 2024, kwamtin samar da tsare-tsare na bankin CBN, ya kara kudin ruwan zuwa 50, wanda ya kai kashi 27.25 daga kashi 26.25.

Bugu da kari, kusan sau biyar duk a 2024, CBN yana kara kudin ruwan, domin yak are hauhawan farashin kaya a kasar.

Har ila yau, Segun ya danganta tsadar kudin makamashi, a matsayin daya daga cikin kalubalen da fannin ke ci gaba da fuskanta, sai dai ya ce, an dan samu ragi a farashin man Dizili, musamman saboda kaddamar da matatar man Dangote.

Ya sanar da cewa, yarjejeniyar da kamfanin NNPCL da matatar man Dangote suka kulla ta sayar da danyen mai a kan farashin Naira, hakan zai taimaka wajen habaka ayyukan masana’antu a zango na hudu na 2024, wanda hakan zai kara taimakawa, wajen raguwar yin amfani da kudaden musaya na ketare.

Shi kuwa Daraktan cibiyar hada-hadar kasuwanci na masu zaman kansu Muda Yusuf ya bayyana cewa, kalubalen da ake fuskanta na samun kudaden musaya, na ci gaba da zamowa fannin karfen kafa.

Ya sanar da cewa, akasarin masu masana’antu a kasar, sun dogara ne kachokam wajen shigo da kayan daga ketare, inda kuma faduwar darajar Naira, ya haifar masu da tsadar gudanar da ayyuansu.

Ya yi nuni da cewa, idan matatar man Dangote ta iya sayen danyen mai a kan farashin Naira hakan zai samarwa da masana’antun sauki.

Kungiyar
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Abin Da Ya Kamata Ka Sani Kan Hannun Jarin Matatar Dangote
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa

MASU ALAKA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas
Tattalin Arziki

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

September 4, 2026
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
Tattalin Arziki

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

September 4, 2026
NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja
Tattalin Arziki

NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja

August 28, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Ganowa Da Maganin Cutar Kiba Fiye Da Kima A Karo Na Farko

Kasar Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Ganowa Da Maganin Cutar Kiba Fiye Da Kima A Karo Na Farko

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.