ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Ya ‘Yantar Da Wasu Ɗaurarru 31 Da Ke Zaman Waƙafi A Gidan Yarin Gusau

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Gwamna Dauda

A  ranar Juma’a ne gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya kai ziyara gidan gyara hali da ke Gusau, inda ya sanya aka saki ɗaurarru 31, kamar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya ya ba shi dama.

 

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa, gwamnan Dauda ya yanke shawarar yin haka ne bisa natsattsen binciken da aka gudanar game da waɗannan masu zaman wakafin.

ADVERTISEMENT
  • Kungiyar Masu Masana’antu Sun Yi Hasashen Matsala Ga Sashen
  • Babban Layin Samar Da Wutar Lantarkin Nijeriya Ya Lalace Sau 7 A 2024

Sanarwar ta ƙara da cewa, tsarin mulki ya ba gwamnoni damar sassauta zaman yari ko ma yafiya ga wadanda ke zaman gidan yari.

 

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Cikin jawabin da ya gabatar a wurin sanya hannu a wannan yafiya, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, ɗaurarru ne masu laifuka daban-daban aka yafe musu domin a ƙarfafa musu gwiwa su zama ‘yan ƙasa nagari masu bin doka da oda.

Gwamna Dauda

“A yau na aiwatar da ikon da kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999, sashe na 212(1) ya ba ni, wanda ke da nufin yaye duk wani ƙunci da damuwa ga masu zaman gidan yari.

“An yanke wannan shawara ne bayan zurfafa binciken da aka yi game da waɗannan ɗaurarru, wanda kuma ya tabbatar da da-na-saninsu bisa abinda suka aikata a baya.

 

“Bugu da ƙari, na amince a bai wa kowanne daga cikinsu Naira 50,000 don su samu abin dogaro da kai bayan fitar su cikin jama’a.

 

“Wannan yana daga cikin ƙoƙarin gwamnati na na rage cunkoso a gidajen yari, musamman a wannan lokacin da muke yawan kamo ‘yan bindiga da masu ba su bayanan sirri.” In ji Gwamna Dauda

 

Bayan zagaya cikin gidan yarin, Gwamna Lawal ya yi alƙawarin bayar da taimakon da ya wajaba ga gidan yarin da ke Gusau.

Gwamna Dauda

Tun farko a nasa jawabin, shugaban Hukumar kula da gidajen gyaran hali ta jihar Zamfara, Dr. Umar Galadima, ya jinjina wa Gwamna Lawal bisa ziyarar da ya kai, tare da yafe wa ɗaurarrun.

Gwamna Dauda
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
Gwamna Dauda
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa
  • Sulaiman
    Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao
  • Sulaiman
    An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

MASU ALAKA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta
Labarai

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Next Post
Wakilin MƊD Ya Nuna Alhini Kan Fashewar Tankar Mai A Jigawa

Wakilin MƊD Ya Nuna Alhini Kan Fashewar Tankar Mai A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026
Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

July 21, 2026
Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.