• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Ya Ziyarci Yankunan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Gummi

by Leadership Hausa
1 year ago
ambaliya

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya kai ziyarar gani da ido zuwa yankunan da ambaliyar ruwa ta shafa a Ƙaramar Hukumar Gummi ta Jihar.

A makon da ya gabata ne mamakon ruwan sama ya haifar da ambaliya a wasu yankunan ƙaramar hukumar Gummi, inda ya lalata gidaje da dama.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce tawagar gwamna Lawal ta fara ne da gaisuwar ban girma ga fadar Mai Martaba Sarkin Gummi, Mai Shari’a Lawal Hassan.

A cewar sanarwar, gwamnan ya zagaya garin Gummi ne domin jajanta wa waɗanda ambaliyar ruwan ta shafa kafin ya wuce garin Gayari domin duba irin ɓarnar da ambaliyar ta yi.

ambaliya

LABARAI MASU NASABA

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Gwamna Lawal ya nuna matuƙar damuwa bayan duba irin ɓarnar da ambaliyar ta yi.

Ya ƙara da cewe, tuni tawagar injiniyoyi suka fara bincike a yankunan domin samun mafita mai ɗorewa.

“A yau, na zo ƙaramar hukumar Gummi ne domin yin jaje tare da gudanar da ziyarar gani da ido a yankunan da ambaliyar ruwa ta shafa a makon jiya.

“Nan da nan bayan na samu labarin faruwar lamarin, sai na aika kwamishinoni biyu domin su kai ziyara kuma su jajanta wa al’ummomin da abin ya shafa.

ambaliya

“Bayan ziyarar mataimakin gwamna, na tura tawagar injiniyoyi domin su duba tare da sanin musabbabin ambaliyar ruwa.

“Yana da muhimmanci a lura cewa na ba da umarnin a fara aiki nan take don daƙile faruwar irin wannna matsalar a nan gaba.

“Ina so in yi amfani da wannan dama wajen sanar da ku cewa na bayar da gudunmawar buhunan abinci guda 10,000 da suka haɗa da shinkafa, masara, da gero, domin raba wa waɗanda ambaliyar ruwan ta shafa. Yanzu haka manyan motocin na kan hanyar Gummi domin a raba wa al’umma.

ambaliya

“Ni kuma a madadin gwamnatin jihar Zamfara, ina tallafa wa waɗanda abin ya shafa da Naira Miliyan 100. Bugu da ƙari, duk waɗanda abin ya shafa, za a raba musu filaye nesa da yankin da ke da haɗari domin su gina sabbin gidaje.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nijeriya
Labarai

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Labarai

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Next Post
Matsin Rayuwa: Duk Da Ƙaruwar Kuɗin Shigar Nijeriya, Akwai Sauran Jan Aiki – Masana

Matsin Rayuwa: Duk Da Ƙaruwar Kuɗin Shigar Nijeriya, Akwai Sauran Jan Aiki - Masana

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
ambaliya

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.