• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kananan Hukumomi 14

by Leadership Hausa and Sulaiman
11 months ago
Gwamna Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya buƙaci sababbin zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomin jihar da su bai wa al’ummarsu fifiko wajen tabbatar da adalci a gudanar da ayyukan raya jihar.

 

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) ta bayyana ’yan takarar jam’iyyar PDP mai mulki a matsayin waɗanda suka lashe zaɓen dukkan kujerun shugabannin ƙananan hukumomi da na kansiloli da aka gudanar a faɗin jihar a ranar Asabar.

  • APEC: Nisan Wuri Ba Ya Hana Sada Zumunci Da Kulla Alheri Tsakanin Sin Da Kasashen Duniya
  • Kasashen Duniya Suna Sa Ran Jin Muryoyin Kasar Sin A Taron Kolin G20

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa an rantsar da zaɓaɓɓun shugabannin ne a yau Lahadi ta hannun Alƙalin Alƙalan Jihar Zamfara, Mai Shari’a Kulu Aliyu, a tsohon zauren majalisa da ke gidan gwamnati a Gusau.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Sanarwar ta ƙara da cewa, a yayin bikin rantsarwar, Gwamna Lawal ya yaba wa shugabannin Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) bisa shirya zabe na gaskiya da adalci.

 

Gwamnan ya jaddada cewa babban burin tsarin ƙananan hukumomi a Nijeriya shi ne kusantar da gwamnati ga jama’a tun daga tushe.

 

“Wannan yana da matuƙar muhimmanci a wannan lokaci, domin ƙananan hukumomi, a matsayinsu na mataki na uku na gwamnati, suna da matuƙar muhimmanci wajen ganin an samar da ingantattun ayyukan da gwamnati mai ci ke yi na ceto jihar daga matsalolin da suka shafi zamantakewa da tattalin arziki da kuma matsalolin tsaro da suka addabi sassan jihar.

 

“Saboda haka, akwai buƙatar haɗin kai tsakanin Majalisun Jihohi da Ƙananan Hukumomi don ƙara habaka cigaba a matakin farko, wanda hakan zai sanya jihar gaba ɗaya ta kasance kan turbar cigaba da wadata.

 

“Ina kira gare ku da ku kalli zabenku a matsayin kira na yi wa al’umma hidima ta hanyar ba da fifiko ga jin daɗin jama’arku da tabbatar da adalci wajen gudanar da ayyukan raya ƙasa. Kamata ya yi a cimma hakan ta hanyar amfani da shirye-shirye daban-daban na zuba jari da sauran tsare-tsare masu kyau da gwamnati mai ci ta bullo da su domin samar da ayyukan yi ga ɗimbin matasan mu, da samar da su da abubuwa masu amfani, da kuma daƙile aikata munanan laifuka da suka addabi jihar. Za a iya cimma hakan ne kawai idan kun rungumi gaskiya, riƙon amana, da taka-tsantsan wajen sarrafa dukiyar al’umma.

 

“Dole ne ku haɗa kai da Gwamnatin Jiha, musamman idan aka yi la’akari da tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima). Gwamnatin Jiha za ta ci gaba da haɗa kai da kansilolinku domin cimma burinmu tare da samar da haɗin kai don ci gaban jiharmu mai daraja”.

 

Gwamna Lawal ya kuma buƙaci zababbun shugabannin da su riƙa hulɗa da al’ummarsu yadda ya kamata.

 

“Ya kamata ku kafa hanyoyin sadarwa masu inganci, waɗanda ke da muhimmanci wajen fahimtar buƙatun mutanen da ku ke yi wa hidima.

Gwamna Lawal

“Ya kamata shugabancin ku ya ƙunshi tausayi da haɗa kai da jama’a ta hanyar tabbatar da cewa babu wani bangare na al’umma da aka bari a baya. Ya kamata a ba da kulawa ta musamman ga mutane mafi rauni – mata, yara, masu buƙatu na musamman, da kuma tsofaffi.

 

“Ina jaddada muku cewa bai kamata ku kebance ayyukanku daga Gwamnatin Jiha ba. Kun kasance wani muhimmin bangare ne na mulki. Don haka, ana sa ran za ku daidaita manufofinku da shirye-shiryenku daidai da abubuwa guda shida na wannan gwamnati: Tsaro, Ilimi, Noma da Tsaron Abinci, Ci gaban Tattalin Arziki, Bangaren Kiwon Lafiya, da Samar da Ababen More Rayuwa.

 

“A dangane da haka, ya zama wajibi ku ƙirƙiri ɗabi’a ta gaskiya da riƙon amana a dukkan harkokin ku. Ku tabbatar cewa kun adana bayanan kuɗinku da kyau kuma ana duba su lokaci-lokaci. Wannan zai ƙara sahihancin gwamnatocinku, ya kuma sa jama’a su aminta da shugabancinku.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja
Manyan Labarai

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Next Post
Muhimman Abubuwa 7 Game Da Raya Huldar Sin Da Amurka

Muhimman Abubuwa 7 Game Da Raya Huldar Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.