• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kananan Hukumomi 14

by Leadership Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kananan Hukumomi 14
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya buƙaci sababbin zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomin jihar da su bai wa al’ummarsu fifiko wajen tabbatar da adalci a gudanar da ayyukan raya jihar.

 

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) ta bayyana ’yan takarar jam’iyyar PDP mai mulki a matsayin waɗanda suka lashe zaɓen dukkan kujerun shugabannin ƙananan hukumomi da na kansiloli da aka gudanar a faɗin jihar a ranar Asabar.

  • APEC: Nisan Wuri Ba Ya Hana Sada Zumunci Da Kulla Alheri Tsakanin Sin Da Kasashen Duniya
  • Kasashen Duniya Suna Sa Ran Jin Muryoyin Kasar Sin A Taron Kolin G20

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa an rantsar da zaɓaɓɓun shugabannin ne a yau Lahadi ta hannun Alƙalin Alƙalan Jihar Zamfara, Mai Shari’a Kulu Aliyu, a tsohon zauren majalisa da ke gidan gwamnati a Gusau.

 

Labarai Masu Nasaba

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

Sanarwar ta ƙara da cewa, a yayin bikin rantsarwar, Gwamna Lawal ya yaba wa shugabannin Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) bisa shirya zabe na gaskiya da adalci.

 

Gwamnan ya jaddada cewa babban burin tsarin ƙananan hukumomi a Nijeriya shi ne kusantar da gwamnati ga jama’a tun daga tushe.

 

“Wannan yana da matuƙar muhimmanci a wannan lokaci, domin ƙananan hukumomi, a matsayinsu na mataki na uku na gwamnati, suna da matuƙar muhimmanci wajen ganin an samar da ingantattun ayyukan da gwamnati mai ci ke yi na ceto jihar daga matsalolin da suka shafi zamantakewa da tattalin arziki da kuma matsalolin tsaro da suka addabi sassan jihar.

 

“Saboda haka, akwai buƙatar haɗin kai tsakanin Majalisun Jihohi da Ƙananan Hukumomi don ƙara habaka cigaba a matakin farko, wanda hakan zai sanya jihar gaba ɗaya ta kasance kan turbar cigaba da wadata.

 

“Ina kira gare ku da ku kalli zabenku a matsayin kira na yi wa al’umma hidima ta hanyar ba da fifiko ga jin daɗin jama’arku da tabbatar da adalci wajen gudanar da ayyukan raya ƙasa. Kamata ya yi a cimma hakan ta hanyar amfani da shirye-shirye daban-daban na zuba jari da sauran tsare-tsare masu kyau da gwamnati mai ci ta bullo da su domin samar da ayyukan yi ga ɗimbin matasan mu, da samar da su da abubuwa masu amfani, da kuma daƙile aikata munanan laifuka da suka addabi jihar. Za a iya cimma hakan ne kawai idan kun rungumi gaskiya, riƙon amana, da taka-tsantsan wajen sarrafa dukiyar al’umma.

 

“Dole ne ku haɗa kai da Gwamnatin Jiha, musamman idan aka yi la’akari da tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima). Gwamnatin Jiha za ta ci gaba da haɗa kai da kansilolinku domin cimma burinmu tare da samar da haɗin kai don ci gaban jiharmu mai daraja”.

 

Gwamna Lawal ya kuma buƙaci zababbun shugabannin da su riƙa hulɗa da al’ummarsu yadda ya kamata.

 

“Ya kamata ku kafa hanyoyin sadarwa masu inganci, waɗanda ke da muhimmanci wajen fahimtar buƙatun mutanen da ku ke yi wa hidima.

Gwamna Lawal

“Ya kamata shugabancin ku ya ƙunshi tausayi da haɗa kai da jama’a ta hanyar tabbatar da cewa babu wani bangare na al’umma da aka bari a baya. Ya kamata a ba da kulawa ta musamman ga mutane mafi rauni – mata, yara, masu buƙatu na musamman, da kuma tsofaffi.

 

“Ina jaddada muku cewa bai kamata ku kebance ayyukanku daga Gwamnatin Jiha ba. Kun kasance wani muhimmin bangare ne na mulki. Don haka, ana sa ran za ku daidaita manufofinku da shirye-shiryenku daidai da abubuwa guda shida na wannan gwamnati: Tsaro, Ilimi, Noma da Tsaron Abinci, Ci gaban Tattalin Arziki, Bangaren Kiwon Lafiya, da Samar da Ababen More Rayuwa.

 

“A dangane da haka, ya zama wajibi ku ƙirƙiri ɗabi’a ta gaskiya da riƙon amana a dukkan harkokin ku. Ku tabbatar cewa kun adana bayanan kuɗinku da kyau kuma ana duba su lokaci-lokaci. Wannan zai ƙara sahihancin gwamnatocinku, ya kuma sa jama’a su aminta da shugabancinku.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan bindigar ZamfaraGwamna Dauda Lawal
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fara Watsa Shirin Zababbun Kalaman Da Shugaba Xi Jinping Ya Fi Kauna A Kasar Brazil

Next Post

Muhimman Abubuwa 7 Game Da Raya Huldar Sin Da Amurka

Related

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

3 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

7 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

10 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

18 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

24 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

1 day ago
Next Post
Muhimman Abubuwa 7 Game Da Raya Huldar Sin Da Amurka

Muhimman Abubuwa 7 Game Da Raya Huldar Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.