ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kananan Hukumomi 14

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Gwamna Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya buƙaci sababbin zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomin jihar da su bai wa al’ummarsu fifiko wajen tabbatar da adalci a gudanar da ayyukan raya jihar.

 

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) ta bayyana ’yan takarar jam’iyyar PDP mai mulki a matsayin waɗanda suka lashe zaɓen dukkan kujerun shugabannin ƙananan hukumomi da na kansiloli da aka gudanar a faɗin jihar a ranar Asabar.

ADVERTISEMENT
  • APEC: Nisan Wuri Ba Ya Hana Sada Zumunci Da Kulla Alheri Tsakanin Sin Da Kasashen Duniya
  • Kasashen Duniya Suna Sa Ran Jin Muryoyin Kasar Sin A Taron Kolin G20

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa an rantsar da zaɓaɓɓun shugabannin ne a yau Lahadi ta hannun Alƙalin Alƙalan Jihar Zamfara, Mai Shari’a Kulu Aliyu, a tsohon zauren majalisa da ke gidan gwamnati a Gusau.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Sanarwar ta ƙara da cewa, a yayin bikin rantsarwar, Gwamna Lawal ya yaba wa shugabannin Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) bisa shirya zabe na gaskiya da adalci.

 

Gwamnan ya jaddada cewa babban burin tsarin ƙananan hukumomi a Nijeriya shi ne kusantar da gwamnati ga jama’a tun daga tushe.

 

“Wannan yana da matuƙar muhimmanci a wannan lokaci, domin ƙananan hukumomi, a matsayinsu na mataki na uku na gwamnati, suna da matuƙar muhimmanci wajen ganin an samar da ingantattun ayyukan da gwamnati mai ci ke yi na ceto jihar daga matsalolin da suka shafi zamantakewa da tattalin arziki da kuma matsalolin tsaro da suka addabi sassan jihar.

 

“Saboda haka, akwai buƙatar haɗin kai tsakanin Majalisun Jihohi da Ƙananan Hukumomi don ƙara habaka cigaba a matakin farko, wanda hakan zai sanya jihar gaba ɗaya ta kasance kan turbar cigaba da wadata.

 

“Ina kira gare ku da ku kalli zabenku a matsayin kira na yi wa al’umma hidima ta hanyar ba da fifiko ga jin daɗin jama’arku da tabbatar da adalci wajen gudanar da ayyukan raya ƙasa. Kamata ya yi a cimma hakan ta hanyar amfani da shirye-shirye daban-daban na zuba jari da sauran tsare-tsare masu kyau da gwamnati mai ci ta bullo da su domin samar da ayyukan yi ga ɗimbin matasan mu, da samar da su da abubuwa masu amfani, da kuma daƙile aikata munanan laifuka da suka addabi jihar. Za a iya cimma hakan ne kawai idan kun rungumi gaskiya, riƙon amana, da taka-tsantsan wajen sarrafa dukiyar al’umma.

 

“Dole ne ku haɗa kai da Gwamnatin Jiha, musamman idan aka yi la’akari da tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima). Gwamnatin Jiha za ta ci gaba da haɗa kai da kansilolinku domin cimma burinmu tare da samar da haɗin kai don ci gaban jiharmu mai daraja”.

 

Gwamna Lawal ya kuma buƙaci zababbun shugabannin da su riƙa hulɗa da al’ummarsu yadda ya kamata.

 

“Ya kamata ku kafa hanyoyin sadarwa masu inganci, waɗanda ke da muhimmanci wajen fahimtar buƙatun mutanen da ku ke yi wa hidima.

Gwamna Lawal

“Ya kamata shugabancin ku ya ƙunshi tausayi da haɗa kai da jama’a ta hanyar tabbatar da cewa babu wani bangare na al’umma da aka bari a baya. Ya kamata a ba da kulawa ta musamman ga mutane mafi rauni – mata, yara, masu buƙatu na musamman, da kuma tsofaffi.

 

“Ina jaddada muku cewa bai kamata ku kebance ayyukanku daga Gwamnatin Jiha ba. Kun kasance wani muhimmin bangare ne na mulki. Don haka, ana sa ran za ku daidaita manufofinku da shirye-shiryenku daidai da abubuwa guda shida na wannan gwamnati: Tsaro, Ilimi, Noma da Tsaron Abinci, Ci gaban Tattalin Arziki, Bangaren Kiwon Lafiya, da Samar da Ababen More Rayuwa.

 

“A dangane da haka, ya zama wajibi ku ƙirƙiri ɗabi’a ta gaskiya da riƙon amana a dukkan harkokin ku. Ku tabbatar cewa kun adana bayanan kuɗinku da kyau kuma ana duba su lokaci-lokaci. Wannan zai ƙara sahihancin gwamnatocinku, ya kuma sa jama’a su aminta da shugabancinku.”

Gwamna Lawal
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
Gwamna Lawal
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
Muhimman Abubuwa 7 Game Da Raya Huldar Sin Da Amurka

Muhimman Abubuwa 7 Game Da Raya Huldar Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.