• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

by Abubakar Abba
2 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya yi kira ga Hukumar Raya Yankin Tafkin Chadi, ta zuba hannun jari a bangaren noman rani a tafkin yankin na Chadi.

Zulum ya sanar da haka ne, a lokacin da yake karbar bakuncin sabbin mahukunta na Hukumar Bunkasa Yankin Tafkin Chadi, a fadar gwamnatin jihar ta Borno da ke Maiduguri, babban birnin jihar.

  • Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu
  • Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Har ila yau, gwamnan ya bukaci zuba hannun jarin, musaman a yankunan Kirenowa, Marte, Gamborun Ngala da kuma Baga.

Zulum ya yi nuni da cewa, zuba hannun jarin zai taimaka matuka da gaske, wajen bunkasa wadataccen abinci da kuma farfado da tattalin arziki a jihar da ma yankin Arewa Maso Gabashin wannan kasa baki- daya.

“Ba zai taba yiwuwa mu ci gaba da dogara kacokan a kan ruwan da muke samu ba, inda ya kara da cewa; bincikenmu ya tabbatar mana da cewa, ruwan da ake samu daga tafkin Chadi na da matukar yawan gaske, wanda idan muka mayar da hankali yadda ya kamata, ko shakka babu, za mu iya jawo ruwan ta hanyar yin amfani da injinoni,” in ji Zulum.

Labarai Masu Nasaba

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Haka zalika, ya kara da cewa; gwamnatinsa ta bayar da kimanin Naira biliyan biyu, domin noma hekta 1,000 na gonaki ta hanyar amfani da na’urar noman rani mai amfani da hasken rana a garin Baga.

Gwamna Zulum ya ci gaba da cewa, kwanan nan ya tura wata tawagar bincike, don yin bincike tare da gano gaskiya zuwa Gamborun Ngala, sannan kuma tawagar ta tabbatar mana da samun albarkatun ruwan karkashin kasa, wadanda za mu iya amfani da su wajen noman rani ta hanyar ban-ruwa.

Kazalika, ya sanar da cewa, an kuma kebe karin wasu Naira biliyan 1.5, domin gudanar da irin wadannan ayyuka a garuruwan Gamborun Ngala da Marte, wadanda a halin yanzu an kusa kammala su baki-daya.

Bugu da kari, ya bayyana cewa; bisa kokarin gwamnatinsa na mayar da hankali wajen farfado da shirin noman rani na Tafkin Chadi ta Kudu, tuni aka fara noma hekta 1,000 a karkashin aikin noma na Baga a kan kudi kimanin Naira biliyan biyu.

Gwaman ya ci gaba da cewa, har ila yau; gwamnatin jihar ta Borno ta samar da hekta 200,000 a Gamboru da kuma wata hekta 200,000 na samar da wutar lantarki a Lamboru ta hanyar amfani da tsarin ban-ruwa, domin farfado da ayyukan noma a fadin yankin baki-daya.

Haka zalika, Zulum ya sanar da cewa, gwamnatinsa ta haka rijiyoyi kusan kimanin 3,000 a Damasak da ke Karamar Hukumar Mobba.

Sannan kuma, ya yi nuni da cewa; wannan ya bai wa manoma da dama damar yin noma a fili mai tsawon kilomita 16, matakin da ya bullo da hanyar noman ruwan karkashin kasa a yankin da a baya ba a saba yin irin sa ba.

Zulum ya kuma yi alkawarin ci gaba da hada kai da hukumar, musamman domin samun nasarar fadada noman a Ngala da Damasak da sabon yankin Marte tare da samar da ababen more rayuwa ga al’ummar yankin da suka dawo yankin da kuma tabbatar da dorewar samar da wadataccen abinci.

Gwamnan ya kuma sanar da cewa, gwamnatinsa na ci gaba da tallafawa wajen farfado da tashar famfunan ruwa da ke Chadi Basin Kirenowa.

A cewarsa, gwamnatinsa na kan kokarin ganin ganin an kafa bataliyar soji a yankin, musamman don inganta tsaro tare da samun zaman lafiya, inda ya kara da cewa; gwamnatin tasa za ta so sanin inda za a iya shiga, sakamakon cewa abubuwan da za a iya samu suna nan.

Ya kara da bayyana cewa, yana ci gaba da tuntubar shugaban kasa da sauran shugabannin sojoji, kan yiwuwar kafa bataliyar soji a Kirenowa da nufin kare tashar famfon.

A nasu jawaban daban-daban tunda farko, shugaban hukumar, Farfesa Abdu Dauda Biu da Manajan Darakta, Alhaji Tijjani Tumsa sun sanar da gwamnan cewa; an kafa sabuwar hukumar ce a ranar 13 ga watan Disamba 2024.

A cewarsu, wannan ziyara na da matukar muhimmancin gaske, duba da cewa; wuraren da ke karkashin kulawarsu, ciki har da madatsar ruwa ta Alau, na samun kulawar da ta dace.

Kazalika, sun kuma jinjina wa Zulum; kan yadda yake gudanar da ayyukansa da kuma jajircewarsa, musamman a wannan bangare na madatsun ruwa da ke wannan jiha.

Har ila yau, shugabancin hukumar ya yi alkawarin hada kai da gwamnatin jihar ta Borno, musamman don samun nasarar aiwatar da wadannan ayyuka da suka shafi noman rani da kiwon dabbobi da kuma kamun kifi a wadannan yankuna.

Haka zalika, sun kuma bukaci goyon bayan Gwamna Zulum, wajen ganin an kammala wannan gyara na madatsar ruwa ta Alau a kan lokaci, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da shi a ‘yan kwanakin baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Noman rani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa

Next Post

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Related

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

1 week ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

2 weeks ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

3 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

3 weeks ago
Next Post
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

LABARAI MASU NASABA

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

August 2, 2025
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

August 2, 2025
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

August 2, 2025
Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

August 2, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.