Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Gwamna Zulum Ya Ziyarci Hukumar Raba-Daidai Ta Kasa

by Muhammad
January 23, 2021
in LABARAI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mustapha Abdullahi,

Gwamnan Jihar Borno, Banagana Umara Zullum ya kai ziyara Hukumar raba-daidai ta kasa, inda ya bukaci Hukumar ta bayar da muhimmanci ga ‘yan asalin Jiharsa wajen daukar aiki.

Gwamna Zullum lokacin da ya kai ziyarar a ranar Litinin, nan take ya bukaci hukumar da ta bayar da muhimmanci ga Jiharsa a duk lokacin da za a dauki aiki a Nijeriya.

Zullum, ya samu gagarumar tarba daga shugaban hukumar da kuma Sakataren hukumar, Dokta Muheeba F. Dankaka da Mohammed Bello Tukur.

Da ta ke mayar da jawabi, Shugabar Hukumar Dokta Muheeba F. Dankaka ta yi alkawarin duba wannan bukata da Gwamna Zulum ya gabatar, inda ta tabbatar da cewa halin da Jihar Borno ke ciki abu ne sananne ga kowa, don haka za a yi wa Jihar Borno adalci a wajen rabon guraben aikin da za a samar.

Shugabar hukumar wacce ta ke tare da daukacin Kwamishinoninta da ke wakiltar Jihohin Nijeriya, duk sun gode wa Gwamna Zulum bisa irin kokarin da yake yi domin ganin rayuwar jama’a ta inganta a kodayaushe.

Wadanda suke a cikin tawagar Gwamnan, sun hada da shugaban ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Farfesa Isa Hussaini Marte, da wasu daga cikin Kwamishinoni, da kuma wasu al’ummar Jihar Borno.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamna Badaru Ya Bukaci Matasa Kan Amfani Da Basirarsu

Next Post

Za Mu Kara Kaimi Wajen Inganta Rayuwa Da Habaka Tattalin Arziki

RelatedPosts

An Yi Wa Buhari Da Osinbajo Allurar Rigakafin Korona

An Yi Wa Buhari Da Osinbajo Allurar Rigakafin Korona

by Sulaiman Ibrahim
52 mins ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim An yi wa Shugaba Muhammadu Buhari da...

Mukabalar

Kotu Ta Dakatar Da Yin Mukabalar Sheikh Abduljabbar Da Malaman Kano.

by Muhammad
6 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Wata kotu a Jihar Kano ta...

Ma'adanai

Masu Hakar Ma’adinai Ba Su Da Alaka a‘Yan Ta’adda -Shugaba

by Muhammad
7 hours ago
0

Daga Idris Aliyu Daudawa, Shugaban kungiyar masu hakar ma'adinai ta  Nijeriya...

Next Post
Rayuwa

Za Mu Kara Kaimi Wajen Inganta Rayuwa Da Habaka Tattalin Arziki

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version