• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Shekarar 2024: Mallam Umar A. Namadi

by Leadership Hausa
7 months ago
in Labarai
0
Gwamnan Shekarar 2024: Mallam Umar A. Namadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mallam Umar Namadi, Gwamnan Jihar Jigawa, ya samu lambar yabo ta LEADERSHIP ta Gwarzon Gwamnan Shekara ta 2024, saboda irin kyakkyawan jagorancinsa wanda ya haɗa da gudanar da mulki mai cike da gaskiya da riƙon amana da samar da ababen more rayuwa da inganta tattalin arziƙi da kuma tallafawa jama’arsa a ɓangarori da dama na rayuwa.

Samun wannan yabo ya nuna yadda jagorancinsa ya haifar da sakamako da ci gaba mai ɗorewa wajen inganta rayuwar al’ummarsa.

  • Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi
  • Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters

Tarihi Da Karatunsa

An haifi Umar Namadi a garin Kafin-Hausa da ke jihar Jigawa, Allah ya albarkaci gidan da ya fito da ilimin addini. Kakansa shi ne Babban Limamin Kafin-Hausa, wanda ya kafa harsashin kyakkyawan jagoranci da sadaukarwa a rayuwarsa. Namadi ya fara karatunsa na firamare a Kafin-Hausa Central Primary School, sannan ya ci gaba a Mallam Madori Teachers’ College, inda ya samu takardar Teachers Grade II Certificate a shekarar 1982.

Bayan haka, Namadi ya rubuta jarrabawar A-Level a 1984, nasarorin da ya samu a fannin ilimi sun ba shi damar shiga Jami’ar Bayero ta Kano, inda ya kammala digiri a ɓangaren Akanta a 1987. Daga baya ya sake samun digiri na biyu a fannin Tsare-tsaren Kasuwanci (Business Administration) (MBA). Kazalika, Namadi mamba ne na ƙungiyoyin ƙwararru Akantoci da suka haɗa da; Institute of Chartered Accountants of Nigeria (ICAN), da Nigerian Institute of Management, da kuma Chartered Institute of Taxation.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Ƙwarewa a Fannin Kuɗi da Kasuwanci

Namadi ya yi aiki a fannonin kuɗi da masana’antu, inda ya fara aikinsa a matsayin babban jami’i mai kula da ƙananan bankuna (Principal Inspection Officer a National Board for Community Banks). Daga nan, ya yi aiki a Kaduna Textiles Limited da kuma rukunin kamfanonin Dangote, inda ya riƙe matsayi daban-daban, har ya zama jami’i mai kula da kuɗi (Financial Controller na Dangote Sugar Refinery) da sauran sassa na rukunin kamfanin Dangote.

Bayan haka, Namadi ya shiga harkokin kasuwanci na kansa, inda ya kafa kamfanonin Ɗanmoɗi Foods Processing Limited da Danmodi Farms Limited. Danmodi Foods ya zama masana’antar sarrafa shinkafa ta farko mai zaman kanta a Jihar Jigawa, wanda ya samar da ayyukan yi da dama ga matasa da kuma bunkasa tattalin arziki.

Shigarsa Siyasa

Namadi ya fara siyasa ne a shekarar 2015 lokacin da ya zama kwamishinan harkokin kuɗi da tsare-tsare na Jihar Jigawa. A wannan matsayi, ya kawo sauye-sauye masu muhimmanci kamar aiwatar da tsarin asusun bai ɗaya (Treasury Single Account (TSA), wanda ya tabbatar da gaskiya da inganci a sarrafa kuɗaɗen jihar. Hakanan, shi ne ya fara tsara takardun kuɗaɗen jihar daga cikin gida, ba tare da dogaro da kamfanoni na waje ba.

Daga 2019 zuwa 2023, ya yi aiki a matsayin Mataimakin Gwamnan Jihar Jigawa, inda ya kasance ginshiƙi kuma abin koyi wajen riƙon gaskiya da amana. Wannan ya tabbatar da karɓuwarsa da amincewar jama’a har aka zaɓe shi a matsayin gwamna a 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Jagoranci a Matsayin Gwamna

A matsayinsa na gwamna, Namadi yana jagorantar jihar bisa hangen nesa, inda ya fi mayar da hankali kan ayyukan more rayuwa da walwalar ma’aikata da noma da ilimi. Gwamna Namadi ya gina hanyoyi da gadoji da dama a faɗin jihar don haɗa yankunan karkara da birane. Wannan ya taimaka wajen bunƙasa tattalin arziƙi da rage cunkoso a wuraren kasuwanci.

Noma: Ya tallafa wa manoma ta hanyar samar da taki mai rahusa da kayan aikin gona da bayar da horo kan sababbin fasahohin noma. Wannan ya ƙara samar da abinci da ayyukan yi ga matasa a jihar.

Ilimi: Namadi ya tabbatar da gyaran makarantu da ɗaukar malamai don inganta tsarin karatu. Hakanan ya kafa Gidauniyar tallafawa ilimi (Educational Foundation) tare da ƙanin sa, Dr Abdullahi Namadi, don tallafa wa ilimin yara.

Tallafi ga Jama’a

Namadi ya kasance gwarzo wajen tallafawa matasa da mata ta hanyoyin samar da jari da damar samun bashi mara kuɗin ruwa. Wannan ya bai wa matasa damar kafa sana’o’in dogaro da kansu, wanda hakan ya rage zaman kashe wando da kuma bunƙasa tattalin arziƙin gida.

Salon Jagoranci:

Namadi ya shahara da mutunci, da kula da jama’a kai tsaye. Ya kasance shugaba mai gaskiya da aiki tuƙuru, wanda hakan ya sa ake ganin sa a matsayin jagora abin koyi.

Tasiri Mai Dorewa

A gwamnatinsa ya tabbatar da samun ci gaba mai dorewa a jihar Jigawa. A yau, jihar Jigawa tana kan tafarki mai kyau na ci gaba, inda Namadi ya gina kyakkyawan yanayi da samar da dama ga matasa da al’ummar jihar baki ɗaya. Wannan lambar yabo ta Gwamnan Shekara tana nuna yadda Namadi ya kasance jagora mai hangen nesa da kyakkyawan shugabanci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiGwamnan JigawaJigawaMallam Umar A. Namadi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kananan Manoma Mata Sun Bukaci Kara Yawan Kasafin Kudin Aikin Noma

Next Post

Gwarzon Shekarar 2024: Barr. Nyesom Ezenwo Wike

Related

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

7 hours ago
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
Labarai

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

9 hours ago
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027
Labarai

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

11 hours ago
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta
Labarai

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

11 hours ago
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

13 hours ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

14 hours ago
Next Post
Gwarzon Shekarar 2024: Barr. Nyesom Ezenwo Wike

Gwarzon Shekarar 2024: Barr. Nyesom Ezenwo Wike

LABARAI MASU NASABA

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.