ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Shekarar 2024: Barr. Nyesom Ezenwo Wike

by Leadership Hausa
2 years ago
Wike

Barrister Nyesom Ezenwo Wike, wanda aka fi sani da “Mr. Project”, ya samu lambar yabo ta Jaridar LEADERSHIP saboda irin gudummawarsa wajen samar da ci gaba ta hanyar samar da ababen more rayuwa ga al’umma a yankunan karkara da birane.

A matsayinsa na ministan babban birnin tarayya, ya kawo sauye-sauye masu yawa, wanda hakan ya sa ya zama jagora mai hangen nesa da jajircewa.

  • Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf
  • Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

Tarihi da Karatunsa

ADVERTISEMENT

An haifi Wike a garin Rumuepirikom, Obio-Akpor da ke Jihar Ribas, a ranar 13 ga Disamba, 1967. Ya karatu a sakandaren gwamnati a Eneka, daga nan ya shiga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Ribas (RSUST), inda ya samu digiri na farko a fannin Shari’a (Law). Bayan haka, ya halarci makarantar koyon aikin lauya (Law School) a shekarar 1997, kuma daga bisani ya samu digiri na biyu a Siyasa da tsare-tsare (Political and Administrative Studies) daga wannan jami’a.

Shigarsa Siyasa

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

Wike ya shiga harkokin siyasa a 1999, lokacin da ya zama shugaban ƙaramar hukumar Obio-Akpor, wanda ya yi shekaru takwas yana mulki. Daga bisani ya zama Shugaban ma’aikata na gwamna Rotimi Amaechi. A shekarar 2011, an naɗa shi ƙaramin Ministan Ilimi a ƙarƙashin gwamnatin Goodluck Jonathan, inda ya kai matsayin Ministan Ilimi mai cikakken iko a 2013.

A matsayinsa na minista, ya kawo sauye-sauye masu mahimmanci a tsarin ilimi a Nijeriya. Ya kuma jagoranci sauyin manufofin da suka inganta damar samun ingantaccen ilimi a duk faɗin Nijeriya.

Gwamnan Jihar Ribas

A ranar 29 ga Mayu, 2015, Wike ya zama Gwamnan Jihar Ribas, inda ya gudanar da ayyukan ci gaba masu tarin yawa. A cikin shekaru takwas na mulkinsa, ya gabatar da ayyukan gine-gine da samar da hanyoyi da inganta lafiya da kuma haɓaka ilimi. Ya kuma tabbatar da biyan albashin ma’aikata akan lokaci da biyan kuɗaɗen ‘yan fansho da tsofaffin ma’aikata. Ya ƙaddamar da ayyukan da suka shafi rayuwar mutanen jiharsa masu muhimmanci, ciki har da samar da hanyoyin mota da gadaje da titunan a birane da karkara. Wannan ya sauya fuskar Jihar Ribas, hakan ya sa al’umma suka amince da jagorancinsa.

Matsayin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT)

An naɗa Wike a matsayin ministan babban birnin tarayya (FCT) a ranar 16 ga Agusta, 2023. Da hawansa wannan matsayi, ya yi duba na musamman kan ayyukan da aka fara amma ba a kammala ba a Abuja. Ya gano manyan matsaloli, musamman waɗanda suka shafi rashin isassun kuɗaɗe, sannan ya ɗauki matakan gaggawa don magance su.

A matsayinsa na minista, Wike ya tabbatar da shugabanci mai kyau wajen bayar da kwangiloli, yana mai cewa ba zai bayar da kwangila ba, ba tare da an tabbatar da kuɗin da ake da su ba a ƙasa ba. Wannan ya kawo gaskiya da inganci a tsarin gudanarwa. Ya gina hanyoyi,

da asibitoci da makarantu a sassa daban-daban na Abuja, ya kuma tabbatar da cewa kowanne yanki ya amfana da shugabancinsa.

Haka kuma, ya sake farfaɗo da filin jirgin saman Abuja na biyu, wanda ya kawo sauƙi ga zirga-zirgar jiragen sama. Ya kuma samar da ingantaccen tsarin sufuri wanda ya rage cunkoso da bunƙasa kasuwanci a Abuja.

Walwalar Ma’aikata da Aikace-aikace

A ƙarƙashin jagorancinsa, Wike ya tabbatar da biyan albashin malaman makaranta da sauran ma’aikata da ya gada a matsayin bashi. Har ila yau, ya inganta walwalar ma’aikata ta hanyar ƙarawa sama da 1,000 girma, wanda hakan ya ƙara musu kwarin gwuiwa. Wike ya tabbatar da cewa ya bai wa sha’anin tsaro fifiko, inda ya haɗa kai da hukumomin tsaro da ƙungiyoyin sa kai don tabbatar da zaman lafiya a Abuja. Wannan ya rage yawan laifuka a birnin, kuma ya ƙara ƙwarin gwuiwar jama’a kan aikin hukumomin tsaro.

Salon Jagorancinsa

Kowa ya san Minista Wike, gwani ne wajen bai wa jama’a kula. Yana ziyartar wuraren gudanar da ayyuka, yana sauraron ƙorafe-ƙorafen jama’a, sannan yana tabbatar da cewa an magance matsalolin da suka taso cikin ƙanƙanin lokaci. Wannan salon jagoranci ya sa jama’a suka gamsu da da irin shugabancinsa.

A yau, Minista Wike ya kafa tarihi a babban birnin tarayya ta fuskar aiyukansa na bunƙasa hanyoyin more rayuwa da walwalar jama’a da tsaro, wanda hakan ya tabbatar da cewa yana da hangen nesa da jajircewa wajen bunƙasa Abuja. Wannan lambar yabo tana nuna yadda ya ke amfani da jagorancinsa wajen kawo ci gaba mai ma’ana ga jama’arsa.

Wike
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Next Post
UBEC

Hukumar Gwamnati Mafi Ƙwazo A Shekarar 2024: Hukumar Ilimin Bai-ɗaya (UBEC)

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.