ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Shekarar 2024: Barr. Nyesom Ezenwo Wike

by Leadership Hausa
2 years ago
Wike

Barrister Nyesom Ezenwo Wike, wanda aka fi sani da “Mr. Project”, ya samu lambar yabo ta Jaridar LEADERSHIP saboda irin gudummawarsa wajen samar da ci gaba ta hanyar samar da ababen more rayuwa ga al’umma a yankunan karkara da birane.

A matsayinsa na ministan babban birnin tarayya, ya kawo sauye-sauye masu yawa, wanda hakan ya sa ya zama jagora mai hangen nesa da jajircewa.

  • Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf
  • Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

Tarihi da Karatunsa

ADVERTISEMENT

An haifi Wike a garin Rumuepirikom, Obio-Akpor da ke Jihar Ribas, a ranar 13 ga Disamba, 1967. Ya karatu a sakandaren gwamnati a Eneka, daga nan ya shiga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Ribas (RSUST), inda ya samu digiri na farko a fannin Shari’a (Law). Bayan haka, ya halarci makarantar koyon aikin lauya (Law School) a shekarar 1997, kuma daga bisani ya samu digiri na biyu a Siyasa da tsare-tsare (Political and Administrative Studies) daga wannan jami’a.

Shigarsa Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Wike ya shiga harkokin siyasa a 1999, lokacin da ya zama shugaban ƙaramar hukumar Obio-Akpor, wanda ya yi shekaru takwas yana mulki. Daga bisani ya zama Shugaban ma’aikata na gwamna Rotimi Amaechi. A shekarar 2011, an naɗa shi ƙaramin Ministan Ilimi a ƙarƙashin gwamnatin Goodluck Jonathan, inda ya kai matsayin Ministan Ilimi mai cikakken iko a 2013.

A matsayinsa na minista, ya kawo sauye-sauye masu mahimmanci a tsarin ilimi a Nijeriya. Ya kuma jagoranci sauyin manufofin da suka inganta damar samun ingantaccen ilimi a duk faɗin Nijeriya.

Gwamnan Jihar Ribas

A ranar 29 ga Mayu, 2015, Wike ya zama Gwamnan Jihar Ribas, inda ya gudanar da ayyukan ci gaba masu tarin yawa. A cikin shekaru takwas na mulkinsa, ya gabatar da ayyukan gine-gine da samar da hanyoyi da inganta lafiya da kuma haɓaka ilimi. Ya kuma tabbatar da biyan albashin ma’aikata akan lokaci da biyan kuɗaɗen ‘yan fansho da tsofaffin ma’aikata. Ya ƙaddamar da ayyukan da suka shafi rayuwar mutanen jiharsa masu muhimmanci, ciki har da samar da hanyoyin mota da gadaje da titunan a birane da karkara. Wannan ya sauya fuskar Jihar Ribas, hakan ya sa al’umma suka amince da jagorancinsa.

Matsayin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT)

An naɗa Wike a matsayin ministan babban birnin tarayya (FCT) a ranar 16 ga Agusta, 2023. Da hawansa wannan matsayi, ya yi duba na musamman kan ayyukan da aka fara amma ba a kammala ba a Abuja. Ya gano manyan matsaloli, musamman waɗanda suka shafi rashin isassun kuɗaɗe, sannan ya ɗauki matakan gaggawa don magance su.

A matsayinsa na minista, Wike ya tabbatar da shugabanci mai kyau wajen bayar da kwangiloli, yana mai cewa ba zai bayar da kwangila ba, ba tare da an tabbatar da kuɗin da ake da su ba a ƙasa ba. Wannan ya kawo gaskiya da inganci a tsarin gudanarwa. Ya gina hanyoyi,

da asibitoci da makarantu a sassa daban-daban na Abuja, ya kuma tabbatar da cewa kowanne yanki ya amfana da shugabancinsa.

Haka kuma, ya sake farfaɗo da filin jirgin saman Abuja na biyu, wanda ya kawo sauƙi ga zirga-zirgar jiragen sama. Ya kuma samar da ingantaccen tsarin sufuri wanda ya rage cunkoso da bunƙasa kasuwanci a Abuja.

Walwalar Ma’aikata da Aikace-aikace

A ƙarƙashin jagorancinsa, Wike ya tabbatar da biyan albashin malaman makaranta da sauran ma’aikata da ya gada a matsayin bashi. Har ila yau, ya inganta walwalar ma’aikata ta hanyar ƙarawa sama da 1,000 girma, wanda hakan ya ƙara musu kwarin gwuiwa. Wike ya tabbatar da cewa ya bai wa sha’anin tsaro fifiko, inda ya haɗa kai da hukumomin tsaro da ƙungiyoyin sa kai don tabbatar da zaman lafiya a Abuja. Wannan ya rage yawan laifuka a birnin, kuma ya ƙara ƙwarin gwuiwar jama’a kan aikin hukumomin tsaro.

Salon Jagorancinsa

Kowa ya san Minista Wike, gwani ne wajen bai wa jama’a kula. Yana ziyartar wuraren gudanar da ayyuka, yana sauraron ƙorafe-ƙorafen jama’a, sannan yana tabbatar da cewa an magance matsalolin da suka taso cikin ƙanƙanin lokaci. Wannan salon jagoranci ya sa jama’a suka gamsu da da irin shugabancinsa.

A yau, Minista Wike ya kafa tarihi a babban birnin tarayya ta fuskar aiyukansa na bunƙasa hanyoyin more rayuwa da walwalar jama’a da tsaro, wanda hakan ya tabbatar da cewa yana da hangen nesa da jajircewa wajen bunƙasa Abuja. Wannan lambar yabo tana nuna yadda ya ke amfani da jagorancinsa wajen kawo ci gaba mai ma’ana ga jama’arsa.

Wike
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi
Manyan Labarai

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati
Labarai

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Next Post
UBEC

Hukumar Gwamnati Mafi Ƙwazo A Shekarar 2024: Hukumar Ilimin Bai-ɗaya (UBEC)

LABARAI MASU NASABA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.