• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Ta Shirya Yi Wa Dabbobi Miliyan 1.8 Rigakafi

by Sani Anwar
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Gwamnatin Kano Ta Shirya Yi Wa Dabbobi Miliyan 1.8 Rigakafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Shirin Jihar Kano na bunkasa noma da kiwo (KSADP), ya jaddada aniyarsa na yi wa akalla shanu miliyan daya da tumaki da akuyoyi dubu 800,000 rigakafi, a shirin rigakafin dabbobi na sheka-shekara da aka saba yi Jihar Kano.

Bankin Musulunci na duniya tare da Cibiyar ‘Libes and Libelihood Funds’ ne za su dauki nauyin shirin kamar yadda suka saba, inda ake sa ran kashe kimanin naira miliyan 160, domin sake bunkasa lafiyar dabbobin tare da kyautata wa makiyaya.

  • Gajiya Ce Ta Sa Na Fadi Yayin Tantance Ni A Majalisa — Balarabe
  • Akwai Yiwuwar Kara Mafi Karancin Albashi Zuwa Dubu 100 Ko 200 – NLC

A sanarwar da mai magana da yawun cibiyar (KSADP) ya fitar, Ameen K. Yassar, wanda aka raba wa ‘yan jaridu, shugaban kula da shirin na Jihar Kano, Malam Ibrahim Garba Muhammad, ne ya bayyana hakan a lokacin bude taron wayar da kan al’umma, musamman makiyaya a kan shirin, wanda aka kaddamar a Fadar Hakimin Kura da ke Karamar Hukumar ta Kura a Jihar Kano.

“Babu shakka, wannan shiri ya kudiri sake kyautata kula rigakafin dabbobi, domin kuwa lafiyar dabbobinku na da kyakkyawar alaka da taku lafiyar tare da habbaka tattalin arzikinmu baki-daya,” in ji Shugaban.

“Babban muhimmin abin da ya hada mu a nan shi ne, sake wayar muku da kai a kan wannan rigakafi ta dabbobi tare da neman hadin guiwar dukkanin shugabanninku, domin ganin wannan shiri ya cimma nasara,” kamar yadda ya bayyana.

Har ila yau, shirin rigakafin na shekara-shekara, ya kunshi wasu shirye-shirye da dama da suka hada da kyautata tare da bunkasa Cibiyar Kadawa ta kyankyasa, gina cibiyar tattara madarar shanu, bunkasa kasuwar dabbobi da sauran makamantansu tare da kyautata rayuwar makiyaya baki-daya.

”Muna sa ran a nan kusa in sha Allahu za mu bayar da aikin katange iyakokin dabbobi a Kano, wanda ko shakka babu hakan zai kawo karshen rikicin manoma da makiyaya a wannan jiha tamu ta Kano”, a cewar tasa.

Hakimin Kura, Dokajin Rano, wanda Alhaji Balarabe Muhammad ya wakilta ya bayyana cewa, daga tsawon shekaru uku zuwa yanzu, ba a samu wani rahoto na bullar wata cuta ko annoba da ta afka wa dabbobinmu ba, sakamakon wannan rigakafi da Cibiyar KSADP ke bai wa dabbobin namu duk shekara.

Haka zalika, ya umarci Dakatai da sauran shugabannin makiyaya da ke zaune a wadannan yankuna, da su fito kwansu da kwarkwatarsu domin rungumar a wannan rigakafi da za a aiwatar a wannan shekara duba da irin muhimmancin da yake da shi.

A nasa tsokacin, a maimakon al’ummar Karamar Hukumar Kura, Malam Zubairu Muhammad cewa ya yi, tuni sun saba da wannan rigakafi, domin kuwa tuni sun ga amfaninta tsawon shekaru uku, saboda haka suna sake bayar da tabbacin bayar da dukkanin hadin kai wajen gudanar da shirin.

“Tuni mun ga amfanin wannan rigakafi da aka gudanar tun a baya, don haka muna godiya ga Bankin Musulunci na duniya tare da Cibiyar ‘Libes and Libelihood Funds’, da rashin gajiyawarsu wajen ci gaba da dawainiya da wannan shiri”.

Shi ma a nasa jawabin, Daraktan Sashen kula da dabbobi na yankin Rano, Dakta Idris Ibrahim ya yi jan hankali a kan muhimmancin wannan rigakafi, inda ya bayar da shawarar cewa, ya kyautu a sanya karnuka cikin wannan rigakafi, tun da dai makiyayan na ta’ammali da su yayin kiwon nasu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsayin Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Na Zuba Dagwalon Nukiliya A Cikin Teku Bai Sauya Ba

Next Post

‘Yancin Kai: Manyan Matsalolin Da Suka Zame Wa Nijeriya Kashin Bakin Tulu

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

2 weeks ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

4 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

4 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 month ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 month ago
Next Post
‘Yancin Kai: Manyan Matsalolin Da Suka Zame Wa Nijeriya Kashin Bakin Tulu

'Yancin Kai: Manyan Matsalolin Da Suka Zame Wa Nijeriya Kashin Bakin Tulu

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Kano

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.