ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Ta Shirya Yi Wa Dabbobi Miliyan 1.8 Rigakafi

by Sani Anwar
3 years ago
Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Shirin Jihar Kano na bunkasa noma da kiwo (KSADP), ya jaddada aniyarsa na yi wa akalla shanu miliyan daya da tumaki da akuyoyi dubu 800,000 rigakafi, a shirin rigakafin dabbobi na sheka-shekara da aka saba yi Jihar Kano.

Bankin Musulunci na duniya tare da Cibiyar ‘Libes and Libelihood Funds’ ne za su dauki nauyin shirin kamar yadda suka saba, inda ake sa ran kashe kimanin naira miliyan 160, domin sake bunkasa lafiyar dabbobin tare da kyautata wa makiyaya.

  • Gajiya Ce Ta Sa Na Fadi Yayin Tantance Ni A Majalisa — Balarabe
  • Akwai Yiwuwar Kara Mafi Karancin Albashi Zuwa Dubu 100 Ko 200 – NLC

A sanarwar da mai magana da yawun cibiyar (KSADP) ya fitar, Ameen K. Yassar, wanda aka raba wa ‘yan jaridu, shugaban kula da shirin na Jihar Kano, Malam Ibrahim Garba Muhammad, ne ya bayyana hakan a lokacin bude taron wayar da kan al’umma, musamman makiyaya a kan shirin, wanda aka kaddamar a Fadar Hakimin Kura da ke Karamar Hukumar ta Kura a Jihar Kano.

“Babu shakka, wannan shiri ya kudiri sake kyautata kula rigakafin dabbobi, domin kuwa lafiyar dabbobinku na da kyakkyawar alaka da taku lafiyar tare da habbaka tattalin arzikinmu baki-daya,” in ji Shugaban.

“Babban muhimmin abin da ya hada mu a nan shi ne, sake wayar muku da kai a kan wannan rigakafi ta dabbobi tare da neman hadin guiwar dukkanin shugabanninku, domin ganin wannan shiri ya cimma nasara,” kamar yadda ya bayyana.

Har ila yau, shirin rigakafin na shekara-shekara, ya kunshi wasu shirye-shirye da dama da suka hada da kyautata tare da bunkasa Cibiyar Kadawa ta kyankyasa, gina cibiyar tattara madarar shanu, bunkasa kasuwar dabbobi da sauran makamantansu tare da kyautata rayuwar makiyaya baki-daya.

”Muna sa ran a nan kusa in sha Allahu za mu bayar da aikin katange iyakokin dabbobi a Kano, wanda ko shakka babu hakan zai kawo karshen rikicin manoma da makiyaya a wannan jiha tamu ta Kano”, a cewar tasa.

Hakimin Kura, Dokajin Rano, wanda Alhaji Balarabe Muhammad ya wakilta ya bayyana cewa, daga tsawon shekaru uku zuwa yanzu, ba a samu wani rahoto na bullar wata cuta ko annoba da ta afka wa dabbobinmu ba, sakamakon wannan rigakafi da Cibiyar KSADP ke bai wa dabbobin namu duk shekara.

Haka zalika, ya umarci Dakatai da sauran shugabannin makiyaya da ke zaune a wadannan yankuna, da su fito kwansu da kwarkwatarsu domin rungumar a wannan rigakafi da za a aiwatar a wannan shekara duba da irin muhimmancin da yake da shi.

A nasa tsokacin, a maimakon al’ummar Karamar Hukumar Kura, Malam Zubairu Muhammad cewa ya yi, tuni sun saba da wannan rigakafi, domin kuwa tuni sun ga amfaninta tsawon shekaru uku, saboda haka suna sake bayar da tabbacin bayar da dukkanin hadin kai wajen gudanar da shirin.

“Tuni mun ga amfanin wannan rigakafi da aka gudanar tun a baya, don haka muna godiya ga Bankin Musulunci na duniya tare da Cibiyar ‘Libes and Libelihood Funds’, da rashin gajiyawarsu wajen ci gaba da dawainiya da wannan shiri”.

Shi ma a nasa jawabin, Daraktan Sashen kula da dabbobi na yankin Rano, Dakta Idris Ibrahim ya yi jan hankali a kan muhimmancin wannan rigakafi, inda ya bayar da shawarar cewa, ya kyautu a sanya karnuka cikin wannan rigakafi, tun da dai makiyayan na ta’ammali da su yayin kiwon nasu.

Kano
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
‘Yancin Kai: Manyan Matsalolin Da Suka Zame Wa Nijeriya Kashin Bakin Tulu

'Yancin Kai: Manyan Matsalolin Da Suka Zame Wa Nijeriya Kashin Bakin Tulu

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.