ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Ta Shirya Yi Wa Dabbobi Miliyan 1.8 Rigakafi

by Sani Anwar
3 years ago
Kano

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Shirin Jihar Kano na bunkasa noma da kiwo (KSADP), ya jaddada aniyarsa na yi wa akalla shanu miliyan daya da tumaki da akuyoyi dubu 800,000 rigakafi, a shirin rigakafin dabbobi na sheka-shekara da aka saba yi Jihar Kano.

Bankin Musulunci na duniya tare da Cibiyar ‘Libes and Libelihood Funds’ ne za su dauki nauyin shirin kamar yadda suka saba, inda ake sa ran kashe kimanin naira miliyan 160, domin sake bunkasa lafiyar dabbobin tare da kyautata wa makiyaya.

  • Gajiya Ce Ta Sa Na Fadi Yayin Tantance Ni A Majalisa — Balarabe
  • Akwai Yiwuwar Kara Mafi Karancin Albashi Zuwa Dubu 100 Ko 200 – NLC

A sanarwar da mai magana da yawun cibiyar (KSADP) ya fitar, Ameen K. Yassar, wanda aka raba wa ‘yan jaridu, shugaban kula da shirin na Jihar Kano, Malam Ibrahim Garba Muhammad, ne ya bayyana hakan a lokacin bude taron wayar da kan al’umma, musamman makiyaya a kan shirin, wanda aka kaddamar a Fadar Hakimin Kura da ke Karamar Hukumar ta Kura a Jihar Kano.

“Babu shakka, wannan shiri ya kudiri sake kyautata kula rigakafin dabbobi, domin kuwa lafiyar dabbobinku na da kyakkyawar alaka da taku lafiyar tare da habbaka tattalin arzikinmu baki-daya,” in ji Shugaban.

“Babban muhimmin abin da ya hada mu a nan shi ne, sake wayar muku da kai a kan wannan rigakafi ta dabbobi tare da neman hadin guiwar dukkanin shugabanninku, domin ganin wannan shiri ya cimma nasara,” kamar yadda ya bayyana.

Har ila yau, shirin rigakafin na shekara-shekara, ya kunshi wasu shirye-shirye da dama da suka hada da kyautata tare da bunkasa Cibiyar Kadawa ta kyankyasa, gina cibiyar tattara madarar shanu, bunkasa kasuwar dabbobi da sauran makamantansu tare da kyautata rayuwar makiyaya baki-daya.

”Muna sa ran a nan kusa in sha Allahu za mu bayar da aikin katange iyakokin dabbobi a Kano, wanda ko shakka babu hakan zai kawo karshen rikicin manoma da makiyaya a wannan jiha tamu ta Kano”, a cewar tasa.

Hakimin Kura, Dokajin Rano, wanda Alhaji Balarabe Muhammad ya wakilta ya bayyana cewa, daga tsawon shekaru uku zuwa yanzu, ba a samu wani rahoto na bullar wata cuta ko annoba da ta afka wa dabbobinmu ba, sakamakon wannan rigakafi da Cibiyar KSADP ke bai wa dabbobin namu duk shekara.

Haka zalika, ya umarci Dakatai da sauran shugabannin makiyaya da ke zaune a wadannan yankuna, da su fito kwansu da kwarkwatarsu domin rungumar a wannan rigakafi da za a aiwatar a wannan shekara duba da irin muhimmancin da yake da shi.

A nasa tsokacin, a maimakon al’ummar Karamar Hukumar Kura, Malam Zubairu Muhammad cewa ya yi, tuni sun saba da wannan rigakafi, domin kuwa tuni sun ga amfaninta tsawon shekaru uku, saboda haka suna sake bayar da tabbacin bayar da dukkanin hadin kai wajen gudanar da shirin.

“Tuni mun ga amfanin wannan rigakafi da aka gudanar tun a baya, don haka muna godiya ga Bankin Musulunci na duniya tare da Cibiyar ‘Libes and Libelihood Funds’, da rashin gajiyawarsu wajen ci gaba da dawainiya da wannan shiri”.

Shi ma a nasa jawabin, Daraktan Sashen kula da dabbobi na yankin Rano, Dakta Idris Ibrahim ya yi jan hankali a kan muhimmancin wannan rigakafi, inda ya bayar da shawarar cewa, ya kyautu a sanya karnuka cikin wannan rigakafi, tun da dai makiyayan na ta’ammali da su yayin kiwon nasu.

Kano
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
‘Yancin Kai: Manyan Matsalolin Da Suka Zame Wa Nijeriya Kashin Bakin Tulu

'Yancin Kai: Manyan Matsalolin Da Suka Zame Wa Nijeriya Kashin Bakin Tulu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.