• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Ta Ayyana Asabar Ɗin Karshe Wata A Matsayin Ranar Tsaftar Muhalli

by Umar Faruk Birnin Kebbi
1 year ago
Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayyana Asabar din kowane jarshe wata a matsayin ranar tsaftar muhalli a jihar.

Gwamnan, ya bayyana haka ne wajen kaddamar da shirin tsaftar muhalli ta kowace karshe wata a jihar.

  • Masu Baje Kolin Kaya Kimanin 300 Za Su Halarci Bikin Kasuwancin Yammacin Afirka A Legas
  • Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Gwamnan wanda mataimakinsa, Sanata Umar Abubakar Tafida ya wakilta, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yanke shawarar sake bullo da kuma karfafa shirin tsaftacce muhalli na wata ne saboda muhimmancinsa ga lafiyar jama’ar.

“Tsaftar muhalli da ruwan sha na da matukar muhimmanci ga jin dadin jama’a don rage cututtukan iska da na ruwa,” in ji shi.

Ya kara da cewa, “Gwamnatina za ta ci gaba da kula da harkokin kiwon lafiya a Jihar Kebbi, a koda yaushe domin tabbatar da cewa al’ummarmu sun kasance ‘yan jiha masu koshin lafiya kuma masu amfani cikin al’umma”.

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

Gwamnan ya ja kunnen jama’a da kada su rika sanya kansu cikin hatsari ta hanyar kazantar muhalli don gujewa cututtuka.

Da yake jawabinsa tun daga farko, Kwamishinan Ma’aikatar Tsaftar Muhalli, Alhaji Musa Muhammad Tungulawa, ya ce gwamnan ya umarci ma’aikatar da ta ci gaba da gudanar da gangamin tsaftace muhalli da wayar da kan jama’a don samun nasara.

“A ranar Asabar din karshe na kowane wata, za a gudanar da atisayen ne a babban birnin jihar, Birnin Kebbi, da kuma dukkan kananan hukumomin 21 na jihar,” in ji shi.

Kwamishinan ya bayyana cewa gwamna Nasir Idris ya ba da fifiko kan harkokin muhalli da kuma samun cikakkiyar tsafta a tsakanin ‘yan jihar.

Sarkin Gwandu, Alhaji Muhammadu Iliyasu Bashar, ya yaba wa gwamnan jihar kan matakin da ya dauka na tabbatar da tsaftar muhalli a jihar.

Sarkin ya umarci jama’a da su kasance masu biyayya da addu’a domin samun nasarar gwamnatin.

“Yin biyayya ga shugabanni yana da su yi aiki, yayin da shugabanci nagari ke ba jama’a kuzari don samun ingantacciyar rayuwa, wasu jihohi da masarautu a wasu wurare suna cikin mawuyacin hali, jihar Kebbi tana cikin kwanciyar hankali da tsaro mai kyau mu ci gaba da zaman lafiya da juna”, in ji Sarkin Gwandu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu
Labarai

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Labarai

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Next Post
Kebbi

Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.