• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Ta Ayyana Asabar Ɗin Karshe Wata A Matsayin Ranar Tsaftar Muhalli

by Umar Faruk Birnin Kebbi
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnatin Kebbi Ta Ayyana Asabar Ɗin Karshe Wata A Matsayin Ranar Tsaftar Muhalli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayyana Asabar din kowane jarshe wata a matsayin ranar tsaftar muhalli a jihar.

Gwamnan, ya bayyana haka ne wajen kaddamar da shirin tsaftar muhalli ta kowace karshe wata a jihar.

  • Masu Baje Kolin Kaya Kimanin 300 Za Su Halarci Bikin Kasuwancin Yammacin Afirka A Legas
  • Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Gwamnan wanda mataimakinsa, Sanata Umar Abubakar Tafida ya wakilta, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yanke shawarar sake bullo da kuma karfafa shirin tsaftacce muhalli na wata ne saboda muhimmancinsa ga lafiyar jama’ar.

“Tsaftar muhalli da ruwan sha na da matukar muhimmanci ga jin dadin jama’a don rage cututtukan iska da na ruwa,” in ji shi.

Ya kara da cewa, “Gwamnatina za ta ci gaba da kula da harkokin kiwon lafiya a Jihar Kebbi, a koda yaushe domin tabbatar da cewa al’ummarmu sun kasance ‘yan jiha masu koshin lafiya kuma masu amfani cikin al’umma”.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Gwamnan ya ja kunnen jama’a da kada su rika sanya kansu cikin hatsari ta hanyar kazantar muhalli don gujewa cututtuka.

Da yake jawabinsa tun daga farko, Kwamishinan Ma’aikatar Tsaftar Muhalli, Alhaji Musa Muhammad Tungulawa, ya ce gwamnan ya umarci ma’aikatar da ta ci gaba da gudanar da gangamin tsaftace muhalli da wayar da kan jama’a don samun nasara.

“A ranar Asabar din karshe na kowane wata, za a gudanar da atisayen ne a babban birnin jihar, Birnin Kebbi, da kuma dukkan kananan hukumomin 21 na jihar,” in ji shi.

Kwamishinan ya bayyana cewa gwamna Nasir Idris ya ba da fifiko kan harkokin muhalli da kuma samun cikakkiyar tsafta a tsakanin ‘yan jihar.

Sarkin Gwandu, Alhaji Muhammadu Iliyasu Bashar, ya yaba wa gwamnan jihar kan matakin da ya dauka na tabbatar da tsaftar muhalli a jihar.

Sarkin ya umarci jama’a da su kasance masu biyayya da addu’a domin samun nasarar gwamnatin.

“Yin biyayya ga shugabanni yana da su yi aiki, yayin da shugabanci nagari ke ba jama’a kuzari don samun ingantacciyar rayuwa, wasu jihohi da masarautu a wasu wurare suna cikin mawuyacin hali, jihar Kebbi tana cikin kwanciyar hankali da tsaro mai kyau mu ci gaba da zaman lafiya da juna”, in ji Sarkin Gwandu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KebbiTsafta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Kin San…Abin Da Ke Lalata Gaban Mace?

Next Post

Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma

Related

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
Labarai

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

34 minutes ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

1 hour ago
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

8 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

8 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

12 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

12 hours ago
Next Post
Kebbi

Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.