• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

by Abubakar Abba
1 year ago
World Bank on glass building. Mirrored sky and city modern facade. Global capital, business, finance, economy, banking and money concept 3D rendering animation.

World Bank on glass building. Mirrored sky and city modern facade. Global capital, business, finance, economy, banking and money concept 3D rendering animation.

Gwamnatin tarayya da Cibiyar Aikin Noma (IITA) da Bankin Duniya da kuma sauran masu ruwa da tsaki a fannin aikin no-ma, sun ayyana kudirinsu na yin hadaka mai karfi a kan aikin noma wanda ke tattare da fasahar zamani.

Sun ayyana yin hakan ne, domin kawo karshen matsalar rashin amfani da fasahar zamani a fadin wannan kasa da kuma Na-hiyar Afirka baki-daya.

  • ‘Yancin Kananan Hukumomi: Kotun Koli Ta Bai Wa Jihohi 36 Kwana 7 Su Kare Kansu
  • Rikicin Masarautar Kano: Lauyoyi Da Alƙalai Sun Tozarta Ɓangaren Shari’a – Shugaban Ƙungiyar Lauyoyi

Har ila yau, wannan kuduri na kunshe ne sakamakon wata ganawa da a aka yi tsakanin Mataimakin Shugaban Kasa, Sana-ta Kashim Shettima da wata tawaga da ta zo daga Cibiyar IITA da Bankin Duniya da kuma Cibiyar Gudanar da Bincken Tsarin Abinci ta Kasa da Kasa (IFPRI).

Kazalika, Mataimakin Shugaban Kasar; a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha ya fitar ya ce; an yi wannan ganawa ce, a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja.

Jawabin Shettima a wajen ganawar ya bayyana cewa, shirin zai mayar da hankali ne kan yadda za a kara samar da wadataccen abinci a fadin kasar nan baki-daya.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Mataimakin ya ce, Cibiyar IITA ta kai matsayin da za ta taimaka wa ba Nijeriya kadai ba, har da ma dukkanin daukacin Nahiyar Afirka, ta yadda za a kara saita tsarin aikin noma da zai iya ju-rewa kowane irin sauyin yanayi tare da kara inganta Irin noma.

Haka zalika, ya yi nuni da cewa; Cibiyar IITA wadda aka kafa ta a shekarar 1967, ta jima tana bayar da gudunmawa ga wannan fanni na aikin noma a Nijeriya, sannan ya kara da cewa; har yanzu muna bukatar wannan gudunmawa tata.

Kazalika, Shettima ya sanar da cewa; nan da 2050, Nijeriya za ta kasance kasa ta uku cikin mafi yawan al’umma a doron kasa.

Ya sanar da cewa, Nahiyar Afirka na fusakantar kalubalen fari, sauyin yanayi da kuma kalubalen rashin tsaro, inda ya kara da cewa, fannin aikin noma na kasar nan na matukar fusakantar koma baya.
Har wa yau, Shettima ya yi kira ga Cibiyar ta IITA, da ta karfafa wannan hadaka, musamman domin samun damar zuba jari a fannin aikin noma ta fuskar kasuwanci.

Sannan kuma, ya bukaci cibiyar ta taimaka wa Nijeriya da ingantaccen Irin shuka na Masara da sauran amfanin gona, musamman Rogo.

Daga nan kuma, ya yaba wa IITA kan yunkurinta na samar da ingantaccen Irin Rogo a yankin kudu maso yamma, inda ya nemi cibiyar da ta kara fadada wannan shiri zuwa sauran kasashen da ke Nahiyar Afirka.
Tun da farko a nasa jawabin, Darakta Janar na Cibiyar IITA, Dakta Simeon Ehui, gode wa Shettima ya yi a kan shugabancinsa da kuma yadda ya mayar da hankali wajen bunkasa fannin aikin noma na kasar nan da kuma goyon bayan da yake bai wa cibiyar.

Dakta Ehui ya kara da cewa, tawagar ta zo Abuja ne; domin ganawa musamman a kan yadda za a sabunta yin hadaka da cibiyar da kuma sauran masu ruwa da tsaki, bisa nufin taimaka wa gwamnain tarayya na kokarinta wajen samar da wadatac-cen abinci a Nijeriya da kuma Nahiyar Afrika baki-daya.

Shi ma a nasa bangaren, Mataimakin Darakta Janar na IITA; Dakta Dashiell Kenton ya bayyana cewa, wannan cibiya tasu na taimaka wa wasu shirye-shiryen gwamnatin tarayya a fannin aikin noma, domin samar da damar kirkiro da wasu ayyukan yi, musamman ga matasan Nijeriya.

Haka zalika, ya yaba da fannin shirin noma don samun riba; wanda Gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Tinubu ta kirkiro da shi, wanda ya yi nuni da cewa; shirin zai sake karfafa guiwar matasan kasar nan da dama.

Kazalika ya sanar da cewa, ta hanyar wannan shiri; cibiyar za ta tallafa wa manoman wannan kasa, musamman kanana ta hanyar ilimatar da su kan yadda za su bunkasa nomansu.

A nasa jawabin, Manajan Sashen Noma da Samar da Abinci na Bankin Duniya, Mista Abel Lufafa ya bayyana cewa, bankin da IITA da sauran masu hadaka; sun ji dadi da irin gudunmawar da Gwamnatin Shugaba Tinubu ke bayarwa, wajen kara habaka fannin aikin noma na Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
bankin duniya

Manoma Za Su Amfana Da Tallafin Dala 25, 000 A Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.