• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

World Bank on glass building. Mirrored sky and city modern facade. Global capital, business, finance, economy, banking and money concept 3D rendering animation.

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya da Cibiyar Aikin Noma (IITA) da Bankin Duniya da kuma sauran masu ruwa da tsaki a fannin aikin no-ma, sun ayyana kudirinsu na yin hadaka mai karfi a kan aikin noma wanda ke tattare da fasahar zamani.

Sun ayyana yin hakan ne, domin kawo karshen matsalar rashin amfani da fasahar zamani a fadin wannan kasa da kuma Na-hiyar Afirka baki-daya.

  • ‘Yancin Kananan Hukumomi: Kotun Koli Ta Bai Wa Jihohi 36 Kwana 7 Su Kare Kansu
  • Rikicin Masarautar Kano: Lauyoyi Da Alƙalai Sun Tozarta Ɓangaren Shari’a – Shugaban Ƙungiyar Lauyoyi

Har ila yau, wannan kuduri na kunshe ne sakamakon wata ganawa da a aka yi tsakanin Mataimakin Shugaban Kasa, Sana-ta Kashim Shettima da wata tawaga da ta zo daga Cibiyar IITA da Bankin Duniya da kuma Cibiyar Gudanar da Bincken Tsarin Abinci ta Kasa da Kasa (IFPRI).

Kazalika, Mataimakin Shugaban Kasar; a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha ya fitar ya ce; an yi wannan ganawa ce, a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja.

Jawabin Shettima a wajen ganawar ya bayyana cewa, shirin zai mayar da hankali ne kan yadda za a kara samar da wadataccen abinci a fadin kasar nan baki-daya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Mataimakin ya ce, Cibiyar IITA ta kai matsayin da za ta taimaka wa ba Nijeriya kadai ba, har da ma dukkanin daukacin Nahiyar Afirka, ta yadda za a kara saita tsarin aikin noma da zai iya ju-rewa kowane irin sauyin yanayi tare da kara inganta Irin noma.

Haka zalika, ya yi nuni da cewa; Cibiyar IITA wadda aka kafa ta a shekarar 1967, ta jima tana bayar da gudunmawa ga wannan fanni na aikin noma a Nijeriya, sannan ya kara da cewa; har yanzu muna bukatar wannan gudunmawa tata.

Kazalika, Shettima ya sanar da cewa; nan da 2050, Nijeriya za ta kasance kasa ta uku cikin mafi yawan al’umma a doron kasa.

Ya sanar da cewa, Nahiyar Afirka na fusakantar kalubalen fari, sauyin yanayi da kuma kalubalen rashin tsaro, inda ya kara da cewa, fannin aikin noma na kasar nan na matukar fusakantar koma baya.
Har wa yau, Shettima ya yi kira ga Cibiyar ta IITA, da ta karfafa wannan hadaka, musamman domin samun damar zuba jari a fannin aikin noma ta fuskar kasuwanci.

Sannan kuma, ya bukaci cibiyar ta taimaka wa Nijeriya da ingantaccen Irin shuka na Masara da sauran amfanin gona, musamman Rogo.

Daga nan kuma, ya yaba wa IITA kan yunkurinta na samar da ingantaccen Irin Rogo a yankin kudu maso yamma, inda ya nemi cibiyar da ta kara fadada wannan shiri zuwa sauran kasashen da ke Nahiyar Afirka.
Tun da farko a nasa jawabin, Darakta Janar na Cibiyar IITA, Dakta Simeon Ehui, gode wa Shettima ya yi a kan shugabancinsa da kuma yadda ya mayar da hankali wajen bunkasa fannin aikin noma na kasar nan da kuma goyon bayan da yake bai wa cibiyar.

Dakta Ehui ya kara da cewa, tawagar ta zo Abuja ne; domin ganawa musamman a kan yadda za a sabunta yin hadaka da cibiyar da kuma sauran masu ruwa da tsaki, bisa nufin taimaka wa gwamnain tarayya na kokarinta wajen samar da wadatac-cen abinci a Nijeriya da kuma Nahiyar Afrika baki-daya.

Shi ma a nasa bangaren, Mataimakin Darakta Janar na IITA; Dakta Dashiell Kenton ya bayyana cewa, wannan cibiya tasu na taimaka wa wasu shirye-shiryen gwamnatin tarayya a fannin aikin noma, domin samar da damar kirkiro da wasu ayyukan yi, musamman ga matasan Nijeriya.

Haka zalika, ya yaba da fannin shirin noma don samun riba; wanda Gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Tinubu ta kirkiro da shi, wanda ya yi nuni da cewa; shirin zai sake karfafa guiwar matasan kasar nan da dama.

Kazalika ya sanar da cewa, ta hanyar wannan shiri; cibiyar za ta tallafa wa manoman wannan kasa, musamman kanana ta hanyar ilimatar da su kan yadda za su bunkasa nomansu.

A nasa jawabin, Manajan Sashen Noma da Samar da Abinci na Bankin Duniya, Mista Abel Lufafa ya bayyana cewa, bankin da IITA da sauran masu hadaka; sun ji dadi da irin gudunmawar da Gwamnatin Shugaba Tinubu ke bayarwa, wajen kara habaka fannin aikin noma na Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AudugaManoman shinkafaNoman alkama
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Baje Kolin Kaya Kimanin 300 Za Su Halarci Bikin Kasuwancin Yammacin Afirka A Legas

Next Post

Manoma Za Su Amfana Da Tallafin Dala 25, 000 A Nasarawa

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

2 days ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

2 days ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 week ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 week ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Next Post
bankin duniya

Manoma Za Su Amfana Da Tallafin Dala 25, 000 A Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.