• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta kuduri aniyar dakatar da shigo da Kifi daga kasashen ketare, wanda aka jima ana yi fitonsa.

A cewar gwamnatin tarayyar, za ta kawo karshin hakan ne ta hanyar bunkasa kamun Kifin a cikin gida Nijeriya.

  • Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
  • An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

Kazalika, za ta yi hakan ne, musamman domin kara karfafa samar da wadataccen abinci a kasar da samar da ayyukan yi da kuma kara karfafa fitar da kayan da ba su shafi fannin mai ba.

Ministan Bunkasa Tattalin Arzikin Teku, Adegboyega Oyetola ne ya sanar da hakan, a yayin wata ganawa da shugabanin kungiyoyin masu kamun Kifi a Abuja.

Ma’aikatar Ministan ce ta shirya ganawar, kan kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi, na saita fannin kamun Kifin a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

“Dole ne kasar nan ta samar da wata sabuwar hanya, domin samar da Kifin da zai wadace ta, wanda hakan zai kuma taimaka matuka wajen rage dogaro da shigo da Kifin daga kasashen waje da kuma kara habaka fannin” in ji Ministan.

Oyetola ya kara da cewa, gwamnatin tarayya ta himmatu kwarai da gaske wajen bai wa fannin goyon bayan da ya dace, musamman ta hanyar yin amfani da tsarin kimiyyar fasahar zamani da kuma zuba makudan kudade a fannin.

Kazalika, ya jaddada cewa; gwamnatin tarayya za ta kara kaimi wajen ganin ana samar da wadataccen Kifi a kasar, musamman domin rage dogaro a kan wadanda ake shigowa da su daga kasashen ketare, duba da cewa; fannin na bayar da gagarumar gudunmawa wajen kara bunkasa tattalin azikin kasar.

Kungiyoyiyon da suka halarci ganawar sun hada; manya-manyan masu ruwa da tsaki a fannin na kamun Kifi, kungiyar masu kamun Kifi ta kasa (FCFN), kungiyar masu kama dabbobin ruwa (TADAN), kungiyar masu kiwon Tarwada ta kasa (CAFAN) da sauran makamantansu.

Babban mai bai wa ministan shawara a fanin yada labarai, Bolaji Akinola, a cikin sanwar da ya bayar; bayan kammala taron ya bayyana cewa; Oyetola ya shaida wa mahalartan cewa, ma’aikatar na kara yin kokari wajen tallafa wa mata da matasa da suka rungumi sana’ar yin kiwon Kifi a karkashin shirye-shiyen da ma’aikatar ta kirkiro.

A cewar ministan, wannan shiri ne na tallafa wa mata da matasa; wanda kuma ya hada da tallafa musu da rance da kayan aiki, musaman don kara musu kwarin gwiwa, domin bayar da tasu gudunmawar wajen kara bunkasa fannin a Nijeriya, wanda kuma ya yi daidai na shirin Shugaban Kasa Bola Tinubu (Renewed Hope Agenda).

“Kara yawan matasan da za su rungumi sana’ar kiwon Kifi, wani babban maki ne, na kara samar da wadataccen abinci a fadin wannan kasa, wanda hakan zai kuma kasance wani mataki ne na rage marasa yin aiki a kasar” a cewar Oyetola.

“Mun mayar da hankali wajen tabatar da cewa, ba a bar mata da matasan kasar nan a baya ba, musamman don ganin an inganta rayuwarsu”, in ji Ministan.

A wajen ganawar, masu ruwa da tsaki a fannnin; sun kuma bijiro da wasu kalubale da ke ci gaba da ci wa fannin tuwo a kwarya.

A cewarsu, kalubalen sun hada da; yawan kamun Kifayen a Kogi, rashin samun rance, karancin kayan adana Kifin da ake adana Kifin bayan kamo su.

Sauran su ne, tsadar abincin da ake ciyar da su, wadanda ake shigo wa da su daga ketare, matsalar safararsu, karbar haraji barkatai, wanda ke sanyawa matasa ba sa iya shiga cikin sana’ar.

Sai dai, Oyetola ya bai wa masu ruwa da tsakin tabbacin cewa, wadannan kalubale da suka bijro da su, ma’aikatar za ta lalubo da mafita a kansu.

A cewarsa,  a yanzu ana kan tattaunawa da Bankin Duniya, musamman domin a samu rancen kudi don tallafa wa masu kiwon Kifin a kasa tare da kuma samar musu da Inshora.

Ministan ya ci gaba da cewa, wannan zai kara tabbatar da nasarar da aka samu a shirin zamani na kamun dabbobin ruwa a Dam din Oyan da kuma sauran yankunan da ma’aikatar tasa ta yi hadaka da ma’aikatar albarkatun ruwa ta tarayya da sauran hukumomin gwamnatin tarayya.

“Wannan ganawa, ba iya nan za ta tsaya ba; amma tamkar yanzu ne aka fara ta, domin za a ci gaba da tattaunawa kan yadda za a ci gaba da habaka fannin,” in ji shi.

Shi kuwa a nasa jawabin, Wellington Omoragbon, Daraktan kula da kamun Kifi da sauran dabbobin ruwa, ya sanar da muhimmancin bukatar kara karfafa hadaka, domin jawo masu son zuba hannun jari a fannin, musamman domin a kara samar da wadataccen Kifi a fadin kasar baki-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Next Post

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Related

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

17 hours ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

18 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

1 week ago
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

1 week ago
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

1 week ago
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

October 4, 2025
Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

October 4, 2025
Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

October 4, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

October 4, 2025
Yadda Za A Magance Amosanin Baki

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

October 4, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

October 4, 2025
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

October 4, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.