ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

by Bello Hamza and Sulaiman
12 months ago
NPA

Tun lokacin da Shuagan kasa Bola Ahemd Tinubu, ya na da NPA Dakta Abubakar Dantsoho, a mukamin Shugaban Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar nan, a 2024, Dantsoho, ya samar da manyan dimbin nasarorin da suka kara ciyar da NPA.

Kazalika, wadannan nasarorin, sun kara samu wa ne, bisa goyon bayan da yake ci gaba da samu daga gun Ministan Bunkasa Tattalin Arziki na Ruwa Adegboyega Oyetola.

Misali, faro ayyukan dala biliyan daya na sake yiwa Tashoshin Jiragen Ruwan kasar kwaskwarima, hakan ya sanya martabar Tashoshin ta sake dawo wa, musamman daga shekarar 2024.

ADVERTISEMENT

Za a iya cewa, Dantsho, na ci gaba da samun wadannan nasarorin ne, saboda zuba hazaka da kwarewar da ya jima yana samar ne, ga a fannin.

Kazalika, hakan ya kuma kara tabbatar da gasa a fannin da kuma kara habaka, tattalin arzikin kasar.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Wani abin karin farin ciki shi ne, yadda masu rauwa da tsaki a fannin, suka jinjinawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, kan yadda ya zabo ya kuma nada Dantsoho, a matsayin shugaban NPA, inda akasarin su, suka yi ittifakin cewa, zabo, bai zama zabar Tumun dare ba, musamman duba da irin dimbin ci gaban da yake ci gaba da samar wa a fannin, a cikin shekara daya kacal.

 

Gyaran Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar:

Tun bayan da ya dare karagar shugabancin NPA Dantsho ya lashi Takon, inganta ayyukan Tashoshin, inda ka fara da tattara bayanan ayyukan da ya kamata ayi da kuma fara yin aikin gadan-gadan, inda aka ware dala bilyan daya, domin fara gyran Tashar Tincan Island, ta Apapa, ta Onne da ke jihar Ribas, ta Warri da kuma ta Kalaba.

 

Aikin Fadada Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar:

A karkashin shugabancin na Dantsoho na NPA, ya dauki sabbin kwararan matakai domin fadada ayyukan na NPA, inda a watan da ya gabata, Dantsoho, ya jagoranci tawagar sauran mahukuntan NPA, kan rattaba hannun yarjejeniyar, dala biliyan daya don bunkasa aikin Tashar Snake Island, don a samar da hekta guda 85, don gudanar da hada-hadar shiyya ta shige da ficen Jiragen Ruwa.

Kazalika, akwai kuma aikin Tashoshin Badagry na Ondo da kuma na Burutu, wadanda a yanzu, suka kai matakin kammala wa.

 

Samar Da Kyakyawan Tsarin Ajiye Kwantaina A Tashshin Jiragen Ruwa:

A karkashin shugabancin sa, NPA ta zama mamba a kungiyar IPCSA, wanda hakan, ya bai wa kasar damar wanzar da aikin NSW.

Dantsoho, ya tabatar da an samar da tsarin gudanar da ayyuka na bai daya, wato NSW wanda shi ne, ake gudanarwa, a daukacin fadin duniya, musamman wajen samun musayara bayanai, na zirga-zirgar kayan da Jirage suka yo dakon su, ko dai ta ruwa, ko ta sama ko kan tudu.

 

Yin Amfani Da Na’urori Don Magance Cunkoson Motoci A Tashoshin Jiragen Ruwa:

Kirkiro da yain amfani da na’urorin rage cunkoson motocin da ke shiga cikin Tashoshin Jiragen Ruwan kasa, da a karkashin shugabancin Dantsoho, hakan ya taimaka matuka wajen rage cunkoso a daukacin Tashoshin kasar, musamman duba da yadda, aka samar da guraren da za a rinka ajiye motocin.

Kazalika, an yi hakan ne, domin a samar saukin gudanar da hada-hadar kasuwanci ta yau da kullum a Tashoshin.

 

Kara Bunkasar Fitar Da Kaya Ketare Da Habakar Kasuwanci:

Sakamakon kara inganta Tashoshin Jiragen Ruwan kasar a karkashin shugabancin Dantosho, hakan ya sanya hada-hadar kasuwancin kasar, a zango na uku na 2024, Nijeriya ta samu Naira tiriliyan 5.81 wadanda suka yi, daidai da dala bilyan 3.7.

Bugu da kari, bisa nasarar da aka samu ta wanzar da tsarin sayar da Danyen Mai da sauran Dangogin Mai kan farashin Naira, da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da umarnin a yi, hakan ya sanya, Nijeriya ta samu damar adana biliyoyin kudaden musaya na kasar waje.

Kazalika, hakan ya sanya, an rage dogaro da shigo Man daga waje, wanda kuma hakan ya kara yawan albarkatun makamashi na kasar, tare da samar da ayyukan yi, na kai tsaye, da wadanda ba na kai tsaye ba.

Hakazalika, a Hukumar NPA a karashin shugabancin Dantsoho, ta sanya batun hadaka da kamfanoni masu zaman kansu wato kan tsarin PPP, wanda hakan ya kara yawan kudaden shigar da take Tarawa.

Shigar Nijeriya Cikin Kungiyar Kula Da Tashoshin Jiragen Ruwa Ta PMAWCA

A lokacin shugabancin sa ne, Nijeriya ta shiga cikin sahun sauran kasashen da ke Afirka ta Yamma na sufurin Jiragen Ruwa, inda aka zabi Dantsoho a matsayin Shugaban kungiyar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa na Afirka Yamma wato PMAWCA.

Kazalika, ta hanyar zabar sa ne, ya sanya tun bayan kafa kungiyar a 1972 aka samu dan Nijeriya na farko, da zama Shugaban kungiyar.

NPA ta taimaka matuka, wajen samar da shawarari kan kara yawan sufurin Jiragen Ruwa daga Tashar Lekki, zuwa sauran kasashen, da ke makwabtaka, da Nijeriya.

 

Kara Samar Da Masu Zuba Hannun Jari:

Duba da irin kwarewar da ya samu, musamman a lokacin da ya rike mukamin Manaja na Tashar Onne, wanda a lokacin ya samar da huddar abotakar kasuwanci a Tashar ta Onne, a kwanna baya Dantsoho ya kai ziyarar aiki, a Tashoshin NPA da ke a Gabashin kasar, musamman idan ya nuna bukatar samar da masu son zuba hannun jari, a Tashohin Ribas, Kalaba da ta Burutu.

Hakan ya sanya, kamfanonin da ke yin dakon Kwantainoni, musamman na yankin Yammacin Afirka wato WACT-APM, suka kadammar da ayyukansu.

Kazalika, an gudanar da aikin ne, bisa hadaka da kamfanin Hapag-Lloyd.

Hakan ya kuma kara bunkasa hada-ahadar kasuwanci a kan lokaci, musamman ga Jiragen da ke sauka a gabashin kasar.

 

Rahoton Kididdigar Ayyuaka A NPA:

Bisa rahoton kididdiga na mahkuntan NPA a 2024, ya nuna cewa, an samu gagarumar ci gaba a bangarori da ban da ban a NPA, wadanda suka hada da; gudanar da ayyuakn zirga-zirgar kananan Jiragen Ruwa da sauransu.

A 2024, NPA ta kara samun yawan Jiragen dakon kaya da ke zuwa Tashoshin Jiragen ruwan kasar, inda suka karu daga kaso kaso 45.1 zuwa kaso 71,213,197, wanda kuma hakan ya nuna cewa, yawan hada-hadar kasuwancin da aka gudanar, sun kara ayyukan na NPA.

Jiragen da ke tsaya wa a Tashar Lekki, sun karu zuwa kaso 2,160.8, inda kuma wadanda ke tsayaw a Tashar Onne, suka karu zuwa kaso 9.4%, sai kuma na Tashar Tin Can Island, da suka karu zuwa kaso 7.3.

 

Samun Karin Jiragen Ruwa Da Ke Zuwa Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar:

Yawan Jiragen Ruwa da ke zuwa Tashoshin sun karu daga kaso 5.6 zuwa kaso 3,791 a 2023, inda kuma a 2024, suka karu zuwa kaso 4,005.

Hakan ya nuna yadda aka samu karin yawan masu yin rijista da suka kai, karin kaso 15.4, wanda hakn yah aura, daga tan na kaya 123,660,278 zuwa tan to142,660,418.

Tashar Lekki ta kasance kan gaba, inda aka yi rijistar Jiragen da ke zuwa Tashar suka karu zuwa kaso 477.6, sai ta Onne, ta samu karin kaso 5.8.

Jimlar Kwantainoni da ake sauke wa a Tashar sun karu zuwa kaso 9.7 a 2024, idan aka kwatatan da na 2023.

Kazalika, karin Kwantaononin da ke fitar da su, sun karu zuwa 53.7 daga kaso 12.2.

Bugu da kari, yawan sauran Kwantainonin da ke fitar da su, sun karu zuwa kaso 136.5.

 

Zirga-Zirgar Kananan Jiragen Ruwa Ta Karu:

Ayyukan zirga-zirgar kanannan Jiragen Ruwa a Tashoshin Jiragenn Ruwan kasar, ya karu zuwa kaso 49.6, inda kuma yawan Jiragen daga 8,956 da ake yin amfani da su a 2023, suka karu zuwa 13,396 a 2024.

Hakazalika, karin wadanda suka yi rijista na GRT, sun karu daga kaso 129.3 zuwa kaso 1,997,163 sai kuma wani karin kaso 4,579,742.

Dantsho ya tabatar da ya daidaita iya lokacin zuwan Jiragen Ruwa ga Tashoshin da kuma lokacin da ya kamata su juya, musamman domin a rage cunkoson Jiragen Ruwa a Tashohin wanda wanda hakan ya sanya aka samu gudanar da ayyuka a Tashoshin da suka kai kaso 1.0.

Musamman a Tashar Lekki wadda ta kasance a cikin kwanuka 2.5 kacal, ake samun Jiragen da ke zuwa suna kuma juyawa, bayan sun sauke kayan da suka yi dako.

Yawan lokutan zuwa da juyawar Jiragen a 2023, ya kai kaso 30.1, wanda a 2024, ya karu zuwa kaso 33.

 

Tabbara Da Walwala Da Jin Dadin Ma’aikata:

Dantsoho ya mayar da hankali wajen inganta jin dadi da walwalar ma’aikan NPA a matsayin daya daga cikin muradun shugabancinsa, musamman ta hanyar yin hadaka da kunyoyin ma’aikatan irinsu, MWUN da kuma SSASGOC.

Hakan ya sanya, kungiyoyin suka kuma yabawa Ministan Bunkasa Tattalin Arziki na Ruwa Adegboyega Oyetola da kuma Dantsoho saboda kawo karshen matsalolin da suka dakele su, na samun ci gaban da ya kamata su samu da sauransu, musamman samun jarrabawar karin girma, a NPA.

 

Samun Jinjina Da Yabo:

Hatta daga gun Dangote da sauran masu ruwa da tsaki da kuma sauran kamfanoni, Dantsoho ya samu yabon su da kuma jinjinar su saboda irin irin kokrin da yake yi na ciyar da NPA gaba.

NPA
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
NPA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B
  • Sulaiman
    CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara

Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

July 11, 2026
Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar  Jamus

Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar Jamus

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ra’ayin Al’umma Game Da Shirin Gwamnati Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 11, 2026
Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.