ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rage Kudin Sufuri Da Kashi 40 Ta Hanyar Amfani Da Motoci Masu Iskar Gas

by Abubakar Abba and Sulaiman
1 year ago
Sufuri

Gwamnatin tarayya ta sanar da shirinta na kara kayan aikin samar da iskar Gas da kuma rage kudin sufirin na iskar Gas, zuwa kaso 40 a cikin dari.

 

Ta bayyana haka ne a yayin da aka rattaba hannun yarkejeniya ta shirin da aka gudanar a Abuja.

ADVERTISEMENT
  • Sin Na Adawa Da Kara Haraji Da EU Ta Yi Kan Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin
  • Dimokuradiyyar Jama’a Da Ta Shafi Matakai Daban Daban Wani Muhimmin Tabbaci Ne Ga Ci Gaban Kasar Sin

A taron rattaba hannun yarjejeniyar, ya samu halartar masu ruwa da tsaki a fannin samar da iskar Gas da kuma wasu wakilan kungiyar kula da surin motoci NURTW da suka fito daga tashoshin motoci na Itakpe, Adabi, da kuma wakilan tasoshin Jiragen kasa da suka fito daga tashar Ajaokuta ta jihar Kogi.

 

LABARAI MASU NASABA

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Daraktan shirin samar da iskar Gas na fadar shugaban kasa Michael Oluwagbemi, a yawabinsa ya jaddda kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi wajen samar da saukin sufuri duba da tashin farashin man fetur.

 

“ A saboda haka ne, shugaban Bola Ahemd Tinubu ya kirkiro da shirin yin amfani da iskar Gas, mai makon dogaro da yin amfani da man fetur a fannin yin sufuri”.

 

Ya ci gaba da cewa, a cikin sabon shirin, kudin sufuri na motar haya da ke daukar matafiya takwas, an rage kudin sufurin daga Naira 12,000 zuwa Naira 7,000.

 

Kazalika, kudin sufurin motar haya da ke daukar matafiya hudu daga Abuja zuwa tashar Jirgen kasa ta Ajaokuta, an rage kudin sufurin daga Naira 13,000 zuwa Naira 8,000, inda ya kara da cewa,tsadar sufuri daga tashar Itakpe zuwa Warri, ta kai Naira 5,000, wanda hakan zai sanya matfiyi ya samu ragin kaso  sama da 40 a cikin dari.

 

Ya ci gaba da cewa, domin a samu nasarar tura  iskar Gas din, tuni a kafa cibiyoyi guda goma a Abuja, Itakpe, da kuma a Ajaokuta, ciki har da a tashoshi shida da hukumar mai ke tafiyar da su da kuma guda biyu a NIPCO.

 

Ya sanar da cewa, ana kuma shirin yin hadaka da tashshi da dama, wanda tuni, aka yi hadaka da kamfanin Bobas, domin a samar da karin kayan aiki a Abuja.

 

Oluwagbemi ya kara da cewa, kamfanin Greenbille na shirin  kaddamar da karin wasu tashohi  17 a daukacin tashoshin da ke a kasar a karshen wannan shekarar.

 

“ Mun kuma yi hadaka da kafanin makamshi na Matrid Energy don a kafa wasu sabbin tashoshi biyar  a jihar Delta da Abuja, tuni kamfanin NNPC, ya kammala aikin wasu tashoshi shida a  Abuja, inda kuma ake jiran a kammala wasu shida a jihar Lagos nan da watan Okutoba”.

 

Ya ce, ana sa ran rage kudin sufurin, zai fara aiki ne a karshen watan Okutobar wannan shekarar.

 

A na sa jawabin, Sakataren kungiyar NURTW reshen tashar Ajaokuta Adeyemo Teslim,  ya bayyana jin dadinsa a kan yin hadakar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur
Tattalin Arziki

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho
Tattalin Arziki

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Next Post
Yadda ‘Yan Bindiga Suka Hana Sallar Juma’a A Katsina

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Hana Sallar Juma’a A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.