• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rage Kudin Sufuri Da Kashi 40 Ta Hanyar Amfani Da Motoci Masu Iskar Gas

by Abubakar Abba and Sulaiman
11 months ago
in Tattalin Arziki
0
Gwamnatin Tarayya Za Ta Rage Kudin Sufuri Da Kashi 40 Ta Hanyar Amfani Da Motoci Masu Iskar Gas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta sanar da shirinta na kara kayan aikin samar da iskar Gas da kuma rage kudin sufirin na iskar Gas, zuwa kaso 40 a cikin dari.

 

Ta bayyana haka ne a yayin da aka rattaba hannun yarkejeniya ta shirin da aka gudanar a Abuja.

  • Sin Na Adawa Da Kara Haraji Da EU Ta Yi Kan Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin
  • Dimokuradiyyar Jama’a Da Ta Shafi Matakai Daban Daban Wani Muhimmin Tabbaci Ne Ga Ci Gaban Kasar Sin

A taron rattaba hannun yarjejeniyar, ya samu halartar masu ruwa da tsaki a fannin samar da iskar Gas da kuma wasu wakilan kungiyar kula da surin motoci NURTW da suka fito daga tashoshin motoci na Itakpe, Adabi, da kuma wakilan tasoshin Jiragen kasa da suka fito daga tashar Ajaokuta ta jihar Kogi.

 

Labarai Masu Nasaba

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Daraktan shirin samar da iskar Gas na fadar shugaban kasa Michael Oluwagbemi, a yawabinsa ya jaddda kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi wajen samar da saukin sufuri duba da tashin farashin man fetur.

 

“ A saboda haka ne, shugaban Bola Ahemd Tinubu ya kirkiro da shirin yin amfani da iskar Gas, mai makon dogaro da yin amfani da man fetur a fannin yin sufuri”.

 

Ya ci gaba da cewa, a cikin sabon shirin, kudin sufuri na motar haya da ke daukar matafiya takwas, an rage kudin sufurin daga Naira 12,000 zuwa Naira 7,000.

 

Kazalika, kudin sufurin motar haya da ke daukar matafiya hudu daga Abuja zuwa tashar Jirgen kasa ta Ajaokuta, an rage kudin sufurin daga Naira 13,000 zuwa Naira 8,000, inda ya kara da cewa,tsadar sufuri daga tashar Itakpe zuwa Warri, ta kai Naira 5,000, wanda hakan zai sanya matfiyi ya samu ragin kaso  sama da 40 a cikin dari.

 

Ya ci gaba da cewa, domin a samu nasarar tura  iskar Gas din, tuni a kafa cibiyoyi guda goma a Abuja, Itakpe, da kuma a Ajaokuta, ciki har da a tashoshi shida da hukumar mai ke tafiyar da su da kuma guda biyu a NIPCO.

 

Ya sanar da cewa, ana kuma shirin yin hadaka da tashshi da dama, wanda tuni, aka yi hadaka da kamfanin Bobas, domin a samar da karin kayan aiki a Abuja.

 

Oluwagbemi ya kara da cewa, kamfanin Greenbille na shirin  kaddamar da karin wasu tashohi  17 a daukacin tashoshin da ke a kasar a karshen wannan shekarar.

 

“ Mun kuma yi hadaka da kafanin makamshi na Matrid Energy don a kafa wasu sabbin tashoshi biyar  a jihar Delta da Abuja, tuni kamfanin NNPC, ya kammala aikin wasu tashoshi shida a  Abuja, inda kuma ake jiran a kammala wasu shida a jihar Lagos nan da watan Okutoba”.

 

Ya ce, ana sa ran rage kudin sufurin, zai fara aiki ne a karshen watan Okutobar wannan shekarar.

 

A na sa jawabin, Sakataren kungiyar NURTW reshen tashar Ajaokuta Adeyemo Teslim,  ya bayyana jin dadinsa a kan yin hadakar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CNG BUSTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Habasha Ta Jinjinawa Masu Zuba Jari Na Kasar Sin

Next Post

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Hana Sallar Juma’a A Katsina

Related

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

2 hours ago
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku
Tattalin Arziki

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

3 hours ago
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

4 hours ago
Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

1 week ago
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta
Tattalin Arziki

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

1 week ago
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
Tattalin Arziki

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

2 weeks ago
Next Post
Yadda ‘Yan Bindiga Suka Hana Sallar Juma’a A Katsina

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Hana Sallar Juma’a A Katsina

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.