• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Yi Aiki Da Manhajoji Domin Tantance Kwazon Ministoci

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Rahotonni
0
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta cimma wasu matakai da ministoci za su gabatar da kwazonsu da suka iya cimmawa a ma’aikatunsu daban-daban, hakan kuma na cikin muhimman bangarori takwas da Shugaban kasa, Bola Tinubu ya sanya a gabasa.

Babban mai bai wa shugaban kasa shawara kan manufofi da tsare-tsare, Hajiya Hadiza Bala-Usman ce ta sanar da hakan a Abuja cikin makon nan.

  • Sin: An Fitar Da Tsarin Tallafin Kudade Domin Bunkasa Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku

Shugaban kasa ya shaida wa ministocinsa cewa tilas a kowace bayan wata uku su gabatar da kwazonsu domin sanin irin azama ko akasinsa da suke yi a bakin aikinsu.

Kazalika, gwamnatin Tinubu ta tsara da fitar da wani manhaja da zai bibiyar kwazon ministoci a ma’aikatunsu, manhajar mai suna ‘Citizens’ Delibery Tracker App’.

‘Yan Nijeriya za su iya amfani da manhajar wajen bayar da bayani ko ra’ayinsu kan manufofi da tsare-tsaren da gwamnati ke musu.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Sannan, hatta ayyukan mazabu da ake bai wa sanatoci da ‘yan majalisu za a dunga bibiya ta wannan manhajar.

Hadiza ta jaddada aniyar gwamnatin Tinubu na gudanar da gwamnati mai cike da gaskiya da fayyace komai ga al’umman kasa.

Ta ce, shugaban kasa ya umarci dukkanin ministoci da dunga zama da al’umman mazabun sanatocin yankunansu a kowace zango na bayan wata uku.

Ta take bayyana sabuwar salon mulkin Tinubu mai suna “Tsarin Mulki Na ‘Yan Kasa”, Hadiza ta ce, tun da dai ministocin nan sun rattaba hannun kan yarjejeniyar yin aiki tukuru, dole ne za a bibiyesu da tantancesu kan muhimman ajandoji guda takwas na Tinubu.

A cewarta, da wannan sabon dabarar bibiyar aikin za a samu cimma muhimman nasarori kan bangarori guda takwas da shugaban kasa ya sanya a gaba wajen ganin ya aiwatar domin kyautata rayuwar al’ummar Nijeriya.

A fadinta kuma, Tinubu ya amince al’umman Nijeriya su san dukkanin abubuwan da gwamnati ke yi da samun damar mu’amalar kai tsaye da ministoci domin himmar da yake da shi wajen gudanar da shugabanci na kwarai ga al’umman kasa.

Ta kara da cewa, sun kuma fito da tsarin gabatar da rahoton ayyuka da zai ba da dama ake samun hakikanin rahotonnin ayyuka da kwazon kowace ma’aikata da rassan gwamnati da kuma hukumominta.

“Muna rungumar tsarin gudanarwa ne na kasa da kasa domin kyautata shugabanci ta hanyar ganowa da bibiyar kwazon ma’aikatu a bangaren aiwatar da manufofi da tsare-tsaren gwamnati,” ta shaida.

Hadiza ta ce jama’an kasa za su iya samun manhajar bibiyar ayyukan da kwazon ne ta shafin yanar gizo kamar haka: app.cdcu.gob.ng.

Ta ce nan da wata guda za a dora manhajar a turakar ‘Google Play Store’ da ‘Apple store’, manhajar zai ba da dama jama’a su san masu kokari da akasin haka.

   


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Sallah

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Rabon Hatsi Tan 42,000

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
Manhajoji
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Ramadan: Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Shirin Rabon Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Rabon Hatsi Tan 42,000

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda YaÆ™in Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin ArziÆ™in Nijeriya

Yadda YaÆ™in Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin ArziÆ™in Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.