• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Sha Sabuwar Damara A Kan Matsalolin Yankin

by Khalid Idris Doya
11 months ago
in Tsaro
0
Gwamnonin Arewa Sun Sha Sabuwar Damara A Kan Matsalolin Yankin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya jaddada damuwar gwamnonin yankin kan yadda matsalar tsaro ke kara tabarbarewa a yankin, ya kuma jaddada kudurinsa na hada kai da masu ruwa da tsaki don magance matsalar yadda ya kamata.

Gwamnan ya tabbatar da hakan ne ranar Litinin yayin da ya karbi cikakken rahoton Gamayyar Kungiyoyin Arewa (CNG) wadda kwamitin kwararru kan matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya ya hada a wani bangare na sakamakon taron tattaunawa da aka gudanar kan matsalar a Abuja.

  • Kakakin Ma’aiktar Tsaron Sin Ya Gabatar Da Yadda Aka Gudanar Da Atisayen Hadin Gwiwa Na Sojojin Sin Da Tanzaniya Da Mozambique
  • Ƙaramin Ministan Tsaro Da Manyan Shugabannin Soji Sun Isa Sokoto Domin Fatattakar ‘Yan Bindiga

Yahaya ya ce rashin tsaro na kara tabarbarewa da rayuwar miliyoyin ‘yan Nijeriya, musamman a fannin noma, lamarin da ya janyo tashin farashin kayan masarufi ba a jihohin Arewa kadai ba, har ma da kasa baki daya.

Ya jaddada cewa gwamnonin sun dukufa wajen ganin sun magance matsalar rashin tsaron da ya addabi yankin, wanda ya haifar da cikas ga harkokin noma, ya kuma ta’azzara hauhawar farashin kayayyakin masarufi da kalubalen tattalin arzikin da kasar nan ke fuskanta.

Ya ce: “A matsayinmu na gwamnoni, mun damu matuka game da matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya, wannan yanki ne da ya fi kowanne yawan al’umma a kasar nan, kuma yana da albarkatun ma’adinai da kasa mai dausayi don noma, karfin noman yankin yana taka rawar gani wajen samar da wadataccen abinci.

Labarai Masu Nasaba

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

“Wani abin takaici shi ne, rashin tsaro da ake fama da shi a halin yanzu yana kawo cikas ga wadannan ayyuka, wanda ke haifar da tsadar kayan masarufi wanda kuma ya shafi dukkan ‘yan Nijeriya, ba kawai na Arewa ba.”

A wani mataki na tinkarar lamarin, kungiyar gwamnonin Arewa karkashin jagorancin Gwamna Inuwa Yahaya, ta bayyana shirin gudanar da wani taro da zai hada dukkan masu ruwa da tsaki da suka hada da shugabanni na da dana yanzu da sarakunan gargajiya da shugabannin tsaro da kungiyoyin fararen fula don tattaunawa tare da aiwatar da dabarun farfado da martabar yankin.

Gwamna Yahaya ya kuma yaba wa shugabannin gamayyar kungiyoyin na Arewa bisa cikakken nazarin da suka yi, yana mai yaba wa da rawar da suke takawa wajen magance matsalolin da yankin ke fuskanta.

Da yake jawabi tun farko, shugaban tawagar kuma shugaban kwamitin kwararru kan harkokin tsaro na kungiyar ta CNG, Bashir Yusuf Ibrahim, ya bayyana cewa rahoton da aka gabatar wa Gwamna Yahayan, sakamako ne na dogon nazarin da aka yi, duba da sassauyawar da ake samu na kalubalen tsaro a Arewacin Nijeriya don samar da hanyoyin magance matsalar.

Da yake karin haske kan wasu abubuwan da rahoton ya kunsa, Bashir ya bayyana wajibcin damawa da kowa wadda kungiyar ta bullo da shi don samar da hadin kai tsakanin masu ruwa da tsaki a sassan Arewacin Nijeriya don magance matsalar rashin tsaro.

Ya ce tuni kungiyar ta mika wannan rahoto ga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ta ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro don daukar mataki a kai.

Da yake yaba wa da zaman lafiya da kwanciyar hankalin da ake samu a Jihar Gombe, jagoran tawagar ya bayyana cewa babu wata jiha da ta tsira daga miyagun laifuka matukar sauran jihohin suna fuskantar matsalar aikata laifuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaArmyGwamnoniPoliceTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fasahohin Kasar Sin Na Taimakawa Afirka Tabbatar Da Wadatar Abinci

Next Post

Goyon Baya Da Addu’ar Iyayena Shi Ne Sirrin Nasarata

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Tsaro

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

1 day ago
Kotu
Tsaro

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

1 day ago
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
Tsaro

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

1 day ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

1 week ago
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi
Labarai

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

2 weeks ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

2 weeks ago
Next Post
Goyon Baya Da Addu’ar Iyayena Shi Ne Sirrin Nasarata

Goyon Baya Da Addu’ar Iyayena Shi Ne Sirrin Nasarata

LABARAI MASU NASABA

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.