• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Sha Sabuwar Damara A Kan Matsalolin Yankin

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Tsaro
0
Gwamnonin Arewa Sun Sha Sabuwar Damara A Kan Matsalolin Yankin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya jaddada damuwar gwamnonin yankin kan yadda matsalar tsaro ke kara tabarbarewa a yankin, ya kuma jaddada kudurinsa na hada kai da masu ruwa da tsaki don magance matsalar yadda ya kamata.

Gwamnan ya tabbatar da hakan ne ranar Litinin yayin da ya karbi cikakken rahoton Gamayyar Kungiyoyin Arewa (CNG) wadda kwamitin kwararru kan matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya ya hada a wani bangare na sakamakon taron tattaunawa da aka gudanar kan matsalar a Abuja.

  • Kakakin Ma’aiktar Tsaron Sin Ya Gabatar Da Yadda Aka Gudanar Da Atisayen Hadin Gwiwa Na Sojojin Sin Da Tanzaniya Da Mozambique
  • Ƙaramin Ministan Tsaro Da Manyan Shugabannin Soji Sun Isa Sokoto Domin Fatattakar ‘Yan Bindiga

Yahaya ya ce rashin tsaro na kara tabarbarewa da rayuwar miliyoyin ‘yan Nijeriya, musamman a fannin noma, lamarin da ya janyo tashin farashin kayan masarufi ba a jihohin Arewa kadai ba, har ma da kasa baki daya.

Ya jaddada cewa gwamnonin sun dukufa wajen ganin sun magance matsalar rashin tsaron da ya addabi yankin, wanda ya haifar da cikas ga harkokin noma, ya kuma ta’azzara hauhawar farashin kayayyakin masarufi da kalubalen tattalin arzikin da kasar nan ke fuskanta.

Ya ce: “A matsayinmu na gwamnoni, mun damu matuka game da matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya, wannan yanki ne da ya fi kowanne yawan al’umma a kasar nan, kuma yana da albarkatun ma’adinai da kasa mai dausayi don noma, karfin noman yankin yana taka rawar gani wajen samar da wadataccen abinci.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

“Wani abin takaici shi ne, rashin tsaro da ake fama da shi a halin yanzu yana kawo cikas ga wadannan ayyuka, wanda ke haifar da tsadar kayan masarufi wanda kuma ya shafi dukkan ‘yan Nijeriya, ba kawai na Arewa ba.”

A wani mataki na tinkarar lamarin, kungiyar gwamnonin Arewa karkashin jagorancin Gwamna Inuwa Yahaya, ta bayyana shirin gudanar da wani taro da zai hada dukkan masu ruwa da tsaki da suka hada da shugabanni na da dana yanzu da sarakunan gargajiya da shugabannin tsaro da kungiyoyin fararen fula don tattaunawa tare da aiwatar da dabarun farfado da martabar yankin.

Gwamna Yahaya ya kuma yaba wa shugabannin gamayyar kungiyoyin na Arewa bisa cikakken nazarin da suka yi, yana mai yaba wa da rawar da suke takawa wajen magance matsalolin da yankin ke fuskanta.

Da yake jawabi tun farko, shugaban tawagar kuma shugaban kwamitin kwararru kan harkokin tsaro na kungiyar ta CNG, Bashir Yusuf Ibrahim, ya bayyana cewa rahoton da aka gabatar wa Gwamna Yahayan, sakamako ne na dogon nazarin da aka yi, duba da sassauyawar da ake samu na kalubalen tsaro a Arewacin Nijeriya don samar da hanyoyin magance matsalar.

Da yake karin haske kan wasu abubuwan da rahoton ya kunsa, Bashir ya bayyana wajibcin damawa da kowa wadda kungiyar ta bullo da shi don samar da hadin kai tsakanin masu ruwa da tsaki a sassan Arewacin Nijeriya don magance matsalar rashin tsaro.

Ya ce tuni kungiyar ta mika wannan rahoto ga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ta ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro don daukar mataki a kai.

Da yake yaba wa da zaman lafiya da kwanciyar hankalin da ake samu a Jihar Gombe, jagoran tawagar ya bayyana cewa babu wata jiha da ta tsira daga miyagun laifuka matukar sauran jihohin suna fuskantar matsalar aikata laifuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaArmyGwamnoniPoliceTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fasahohin Kasar Sin Na Taimakawa Afirka Tabbatar Da Wadatar Abinci

Next Post

Goyon Baya Da Addu’ar Iyayena Shi Ne Sirrin Nasarata

Related

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

3 days ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

3 days ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

1 week ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

1 week ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

1 week ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

2 weeks ago
Next Post
Goyon Baya Da Addu’ar Iyayena Shi Ne Sirrin Nasarata

Goyon Baya Da Addu’ar Iyayena Shi Ne Sirrin Nasarata

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.