ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Sha Sabuwar Damara A Kan Matsalolin Yankin

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Arewa

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya jaddada damuwar gwamnonin yankin kan yadda matsalar tsaro ke kara tabarbarewa a yankin, ya kuma jaddada kudurinsa na hada kai da masu ruwa da tsaki don magance matsalar yadda ya kamata.

Gwamnan ya tabbatar da hakan ne ranar Litinin yayin da ya karbi cikakken rahoton Gamayyar Kungiyoyin Arewa (CNG) wadda kwamitin kwararru kan matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya ya hada a wani bangare na sakamakon taron tattaunawa da aka gudanar kan matsalar a Abuja.

  • Kakakin Ma’aiktar Tsaron Sin Ya Gabatar Da Yadda Aka Gudanar Da Atisayen Hadin Gwiwa Na Sojojin Sin Da Tanzaniya Da Mozambique
  • Ƙaramin Ministan Tsaro Da Manyan Shugabannin Soji Sun Isa Sokoto Domin Fatattakar ‘Yan Bindiga

Yahaya ya ce rashin tsaro na kara tabarbarewa da rayuwar miliyoyin ‘yan Nijeriya, musamman a fannin noma, lamarin da ya janyo tashin farashin kayan masarufi ba a jihohin Arewa kadai ba, har ma da kasa baki daya.

ADVERTISEMENT

Ya jaddada cewa gwamnonin sun dukufa wajen ganin sun magance matsalar rashin tsaron da ya addabi yankin, wanda ya haifar da cikas ga harkokin noma, ya kuma ta’azzara hauhawar farashin kayayyakin masarufi da kalubalen tattalin arzikin da kasar nan ke fuskanta.

Ya ce: “A matsayinmu na gwamnoni, mun damu matuka game da matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya, wannan yanki ne da ya fi kowanne yawan al’umma a kasar nan, kuma yana da albarkatun ma’adinai da kasa mai dausayi don noma, karfin noman yankin yana taka rawar gani wajen samar da wadataccen abinci.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

“Wani abin takaici shi ne, rashin tsaro da ake fama da shi a halin yanzu yana kawo cikas ga wadannan ayyuka, wanda ke haifar da tsadar kayan masarufi wanda kuma ya shafi dukkan ‘yan Nijeriya, ba kawai na Arewa ba.”

A wani mataki na tinkarar lamarin, kungiyar gwamnonin Arewa karkashin jagorancin Gwamna Inuwa Yahaya, ta bayyana shirin gudanar da wani taro da zai hada dukkan masu ruwa da tsaki da suka hada da shugabanni na da dana yanzu da sarakunan gargajiya da shugabannin tsaro da kungiyoyin fararen fula don tattaunawa tare da aiwatar da dabarun farfado da martabar yankin.

Gwamna Yahaya ya kuma yaba wa shugabannin gamayyar kungiyoyin na Arewa bisa cikakken nazarin da suka yi, yana mai yaba wa da rawar da suke takawa wajen magance matsalolin da yankin ke fuskanta.

Da yake jawabi tun farko, shugaban tawagar kuma shugaban kwamitin kwararru kan harkokin tsaro na kungiyar ta CNG, Bashir Yusuf Ibrahim, ya bayyana cewa rahoton da aka gabatar wa Gwamna Yahayan, sakamako ne na dogon nazarin da aka yi, duba da sassauyawar da ake samu na kalubalen tsaro a Arewacin Nijeriya don samar da hanyoyin magance matsalar.

Da yake karin haske kan wasu abubuwan da rahoton ya kunsa, Bashir ya bayyana wajibcin damawa da kowa wadda kungiyar ta bullo da shi don samar da hadin kai tsakanin masu ruwa da tsaki a sassan Arewacin Nijeriya don magance matsalar rashin tsaro.

Ya ce tuni kungiyar ta mika wannan rahoto ga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ta ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro don daukar mataki a kai.

Da yake yaba wa da zaman lafiya da kwanciyar hankalin da ake samu a Jihar Gombe, jagoran tawagar ya bayyana cewa babu wata jiha da ta tsira daga miyagun laifuka matukar sauran jihohin suna fuskantar matsalar aikata laifuka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

October 12, 2025
Next Post
Goyon Baya Da Addu’ar Iyayena Shi Ne Sirrin Nasarata

Goyon Baya Da Addu’ar Iyayena Shi Ne Sirrin Nasarata

LABARAI MASU NASABA

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025
Tinubu

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.