ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Sha Sabuwar Damara A Kan Matsalolin Yankin

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Arewa

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya jaddada damuwar gwamnonin yankin kan yadda matsalar tsaro ke kara tabarbarewa a yankin, ya kuma jaddada kudurinsa na hada kai da masu ruwa da tsaki don magance matsalar yadda ya kamata.

Gwamnan ya tabbatar da hakan ne ranar Litinin yayin da ya karbi cikakken rahoton Gamayyar Kungiyoyin Arewa (CNG) wadda kwamitin kwararru kan matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya ya hada a wani bangare na sakamakon taron tattaunawa da aka gudanar kan matsalar a Abuja.

  • Kakakin Ma’aiktar Tsaron Sin Ya Gabatar Da Yadda Aka Gudanar Da Atisayen Hadin Gwiwa Na Sojojin Sin Da Tanzaniya Da Mozambique
  • Ƙaramin Ministan Tsaro Da Manyan Shugabannin Soji Sun Isa Sokoto Domin Fatattakar ‘Yan Bindiga

Yahaya ya ce rashin tsaro na kara tabarbarewa da rayuwar miliyoyin ‘yan Nijeriya, musamman a fannin noma, lamarin da ya janyo tashin farashin kayan masarufi ba a jihohin Arewa kadai ba, har ma da kasa baki daya.

ADVERTISEMENT

Ya jaddada cewa gwamnonin sun dukufa wajen ganin sun magance matsalar rashin tsaron da ya addabi yankin, wanda ya haifar da cikas ga harkokin noma, ya kuma ta’azzara hauhawar farashin kayayyakin masarufi da kalubalen tattalin arzikin da kasar nan ke fuskanta.

Ya ce: “A matsayinmu na gwamnoni, mun damu matuka game da matsalar tsaro a Arewacin Nijeriya, wannan yanki ne da ya fi kowanne yawan al’umma a kasar nan, kuma yana da albarkatun ma’adinai da kasa mai dausayi don noma, karfin noman yankin yana taka rawar gani wajen samar da wadataccen abinci.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

“Wani abin takaici shi ne, rashin tsaro da ake fama da shi a halin yanzu yana kawo cikas ga wadannan ayyuka, wanda ke haifar da tsadar kayan masarufi wanda kuma ya shafi dukkan ‘yan Nijeriya, ba kawai na Arewa ba.”

A wani mataki na tinkarar lamarin, kungiyar gwamnonin Arewa karkashin jagorancin Gwamna Inuwa Yahaya, ta bayyana shirin gudanar da wani taro da zai hada dukkan masu ruwa da tsaki da suka hada da shugabanni na da dana yanzu da sarakunan gargajiya da shugabannin tsaro da kungiyoyin fararen fula don tattaunawa tare da aiwatar da dabarun farfado da martabar yankin.

Gwamna Yahaya ya kuma yaba wa shugabannin gamayyar kungiyoyin na Arewa bisa cikakken nazarin da suka yi, yana mai yaba wa da rawar da suke takawa wajen magance matsalolin da yankin ke fuskanta.

Da yake jawabi tun farko, shugaban tawagar kuma shugaban kwamitin kwararru kan harkokin tsaro na kungiyar ta CNG, Bashir Yusuf Ibrahim, ya bayyana cewa rahoton da aka gabatar wa Gwamna Yahayan, sakamako ne na dogon nazarin da aka yi, duba da sassauyawar da ake samu na kalubalen tsaro a Arewacin Nijeriya don samar da hanyoyin magance matsalar.

Da yake karin haske kan wasu abubuwan da rahoton ya kunsa, Bashir ya bayyana wajibcin damawa da kowa wadda kungiyar ta bullo da shi don samar da hadin kai tsakanin masu ruwa da tsaki a sassan Arewacin Nijeriya don magance matsalar rashin tsaro.

Ya ce tuni kungiyar ta mika wannan rahoto ga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ta ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro don daukar mataki a kai.

Da yake yaba wa da zaman lafiya da kwanciyar hankalin da ake samu a Jihar Gombe, jagoran tawagar ya bayyana cewa babu wata jiha da ta tsira daga miyagun laifuka matukar sauran jihohin suna fuskantar matsalar aikata laifuka.

Arewa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
Next Post
Goyon Baya Da Addu’ar Iyayena Shi Ne Sirrin Nasarata

Goyon Baya Da Addu’ar Iyayena Shi Ne Sirrin Nasarata

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.