• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Ɗan Siyasar Shekarar 2024: Adams Oshiomhole (CON)

by Muhammad
7 months ago
in Labarai
0
Gwarzon Ɗan Siyasar Shekarar 2024: Adams Oshiomhole (CON)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Adams Oshiomhole fitaccen ɗan siyasa ne a Nijeriya, kuma Tsohon Gwamnan Jihar Edo. Yanzu haka, shi ne Sanatan da ke wakiltar Edo ta Arewa. Jagoranci da ƙwarewarsa a fannin siyasa sun taka rawar gani sosai a siyasar Nijeriya, musamman a zaɓen Gwamnan Jihar Edo na 2024, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da nasarar ɗan takarar Jam’iyyar APC, Sanata Monday Okpebholo.

An haifi Oshiomhole a ranar 4 ga watan Afrilun 1952, a Jihar Edo. Ya fara aikinsa a matsayin mai fafutukar kare haƙƙin ma’aikata, inda ya zama Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC). A lokacin da yake shugabancin NLC, ya tsaya tsayin daka wajen kare haƙƙin ma’aikata, ya kuma jagoranci tattaunawa kan muhimman manufofi, wanda ya sa aka san shi a matsayin jagora mai tsayin daka.

  • Ɗangote Ne Gwarzon Jaridar LEADERSHIP Na Shekara Ta 2024
  • Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf

A shekarar 2008, ya zama Gwamnan Jihar Edo, bayan hukuncin kotu. A lokacin mulkinsa, ya mayar da hankali kan inganta ababen more rayuwa da kiwon lafiya da ilimi, ciki har da shahararren shirinsa na “Red Roof Revolution,” wanda ya gyara makarantu a faɗin jihar. Salon mulkinsa na kula da jama’a ya sa ake girmama shi sosai.

A shekarar 2018, an naɗa shi shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, inda ya tallafa wa jam’iyyar kuma ya goyi bayan gwamnatin Shugaba Buhari. Duk da ƙalubalen cikin gida, jagorancin Oshiomhole ya taimaka wajen samun nasarori a zaɓuɓɓuka masu muhimmanci.

A matsayinsa na Sanata, ya mayar da hankali kan ci gaban ababen more rayuwa, bai wa matasa dama, da samar da ayyukan yi mazaɓarsa. Har yanzu yana da tasiri a wajen al’amur ƙasa da na yankinsa, inda yake amfani da ƙwarewarsa a fannin mulki da fafutuka.

Labarai Masu Nasaba

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Sadaukarwar Oshiomhole wajen yi wa jama’a hidima da rawar da ya taka a fagen siyasar Nijeriya ya sa ya cancanci zama Gwarzon Ɗan Siyasa na Shekarar 2024 na Jaridar Leadership.

Tsarin shugabancinsa na samar da ci gaba da bai wa al’umma ƙwarin gwiwa yana matuƙar tasiri a ƙasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiAdams Oshiomhole
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf

Next Post

Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta

Related

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

6 minutes ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

36 minutes ago
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano
Labarai

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

1 hour ago
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

5 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

6 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

17 hours ago
Next Post
Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta

Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta

LABARAI MASU NASABA

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.