ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Ɗan Siyasar Shekarar 2024: Adams Oshiomhole (CON)

by Muhammad
2 years ago
Adams Oshiomhole

Adams Oshiomhole fitaccen ɗan siyasa ne a Nijeriya, kuma Tsohon Gwamnan Jihar Edo. Yanzu haka, shi ne Sanatan da ke wakiltar Edo ta Arewa. Jagoranci da ƙwarewarsa a fannin siyasa sun taka rawar gani sosai a siyasar Nijeriya, musamman a zaɓen Gwamnan Jihar Edo na 2024, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da nasarar ɗan takarar Jam’iyyar APC, Sanata Monday Okpebholo.

An haifi Oshiomhole a ranar 4 ga watan Afrilun 1952, a Jihar Edo. Ya fara aikinsa a matsayin mai fafutukar kare haƙƙin ma’aikata, inda ya zama Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC). A lokacin da yake shugabancin NLC, ya tsaya tsayin daka wajen kare haƙƙin ma’aikata, ya kuma jagoranci tattaunawa kan muhimman manufofi, wanda ya sa aka san shi a matsayin jagora mai tsayin daka.

  • Ɗangote Ne Gwarzon Jaridar LEADERSHIP Na Shekara Ta 2024
  • Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf

A shekarar 2008, ya zama Gwamnan Jihar Edo, bayan hukuncin kotu. A lokacin mulkinsa, ya mayar da hankali kan inganta ababen more rayuwa da kiwon lafiya da ilimi, ciki har da shahararren shirinsa na “Red Roof Revolution,” wanda ya gyara makarantu a faɗin jihar. Salon mulkinsa na kula da jama’a ya sa ake girmama shi sosai.

ADVERTISEMENT

A shekarar 2018, an naɗa shi shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, inda ya tallafa wa jam’iyyar kuma ya goyi bayan gwamnatin Shugaba Buhari. Duk da ƙalubalen cikin gida, jagorancin Oshiomhole ya taimaka wajen samun nasarori a zaɓuɓɓuka masu muhimmanci.

A matsayinsa na Sanata, ya mayar da hankali kan ci gaban ababen more rayuwa, bai wa matasa dama, da samar da ayyukan yi mazaɓarsa. Har yanzu yana da tasiri a wajen al’amur ƙasa da na yankinsa, inda yake amfani da ƙwarewarsa a fannin mulki da fafutuka.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Sadaukarwar Oshiomhole wajen yi wa jama’a hidima da rawar da ya taka a fagen siyasar Nijeriya ya sa ya cancanci zama Gwarzon Ɗan Siyasa na Shekarar 2024 na Jaridar Leadership.

Tsarin shugabancinsa na samar da ci gaba da bai wa al’umma ƙwarin gwiwa yana matuƙar tasiri a ƙasar nan.

Adams Oshiomhole
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta

Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.