ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Ɗan Siyasar Shekarar 2024: Adams Oshiomhole (CON)

by Muhammad
2 years ago
Adams Oshiomhole

Adams Oshiomhole fitaccen ɗan siyasa ne a Nijeriya, kuma Tsohon Gwamnan Jihar Edo. Yanzu haka, shi ne Sanatan da ke wakiltar Edo ta Arewa. Jagoranci da ƙwarewarsa a fannin siyasa sun taka rawar gani sosai a siyasar Nijeriya, musamman a zaɓen Gwamnan Jihar Edo na 2024, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da nasarar ɗan takarar Jam’iyyar APC, Sanata Monday Okpebholo.

An haifi Oshiomhole a ranar 4 ga watan Afrilun 1952, a Jihar Edo. Ya fara aikinsa a matsayin mai fafutukar kare haƙƙin ma’aikata, inda ya zama Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC). A lokacin da yake shugabancin NLC, ya tsaya tsayin daka wajen kare haƙƙin ma’aikata, ya kuma jagoranci tattaunawa kan muhimman manufofi, wanda ya sa aka san shi a matsayin jagora mai tsayin daka.

  • Ɗangote Ne Gwarzon Jaridar LEADERSHIP Na Shekara Ta 2024
  • Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf

A shekarar 2008, ya zama Gwamnan Jihar Edo, bayan hukuncin kotu. A lokacin mulkinsa, ya mayar da hankali kan inganta ababen more rayuwa da kiwon lafiya da ilimi, ciki har da shahararren shirinsa na “Red Roof Revolution,” wanda ya gyara makarantu a faɗin jihar. Salon mulkinsa na kula da jama’a ya sa ake girmama shi sosai.

ADVERTISEMENT

A shekarar 2018, an naɗa shi shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, inda ya tallafa wa jam’iyyar kuma ya goyi bayan gwamnatin Shugaba Buhari. Duk da ƙalubalen cikin gida, jagorancin Oshiomhole ya taimaka wajen samun nasarori a zaɓuɓɓuka masu muhimmanci.

A matsayinsa na Sanata, ya mayar da hankali kan ci gaban ababen more rayuwa, bai wa matasa dama, da samar da ayyukan yi mazaɓarsa. Har yanzu yana da tasiri a wajen al’amur ƙasa da na yankinsa, inda yake amfani da ƙwarewarsa a fannin mulki da fafutuka.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

Sadaukarwar Oshiomhole wajen yi wa jama’a hidima da rawar da ya taka a fagen siyasar Nijeriya ya sa ya cancanci zama Gwarzon Ɗan Siyasa na Shekarar 2024 na Jaridar Leadership.

Tsarin shugabancinsa na samar da ci gaba da bai wa al’umma ƙwarin gwiwa yana matuƙar tasiri a ƙasar nan.

Adams Oshiomhole
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato
Labarai

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno
Manyan Labarai

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Next Post
Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta

Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.