ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf

by Leadership Hausa
2 years ago
Gwamna

Alhaji Abba Kabir Yusuf ya samu lambar yabo ta Gwarzon Gwamnan Shekara ta 2024 ta Jaridar Leadership, saboda gagarumin aikin da ya yi a fannin ilimi da sauran muhimman ɓangarorin ci gaba a Jihar Kano. 

Gwamnatinsa ta ayyana dokar ta-ɓaci kan ilimi tare da ware kashi 31 na kasafin kuɗin jihar na Naira biliyan 570, kwatankwacin Naira biliyan 165.4, a ɓangaren ilimi. Wannan matakin na nufin magance matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta, wadda Kano ce ke kan gaba na mafi yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya, da kuma bai wa yara marasa galihu damar samun ingantaccen ilimi.

  • Gwamna Yusuf Ya Mika Motocin Bas Na CNG Guda 10 Ga Kungiyar NLC Reshen Kano
  • Kano Ta Kaddamar Da Cibiyar Tafi-da-gidanka Ta Farko A Nijeriya Don Yi Wa Motoci Lasisi

Gwamna Yusuf ya yi sabbin gine-gine a makarantu, ya samar da kujeru da tebura da sauran kayan karatu. Haka kuma, gwamnatinsa ta bayar da tallafin karatu ga matasa maza da mata da yawa don yin karatu a ƙasashen waje, don tabbatar da cewa ilimi ya zama ginshiƙin ci gaban jihar.

ADVERTISEMENT

Shahararsa da kalaman “ilimi, ilimi, ilimi” sun tabbatar da cewa ɓangaren ilimi shi ne abin da ya fi bai wa fifiko.

An haifi Alhaji Abba Kabir Yusuf a gidan Sarautar Fulanin Sulluɓawa, wanda suke wani tsagi ne daga sarakunan Masarautar Kano. Ya yi ƙuruciyarsa a Gaya, a hannun kakansa, Alhaji Yusuf Bashari, Hakimin Gaya. Ya yi karatunsa na Firamare da Sakandire a Kano kafin samun difiloma a Fannin Injiniyan Ruwa da Muhalli a Kwalejin Fasaha ta Mubi da Kaduna Polytechnic.

LABARAI MASU NASABA

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Daga baya, Gwamna Yusuf ya samu shaidar digiri a fannin gudanarwa a Jami’ar Bayero ta Kano. Abba Kabir Yusuf ya fara aikinsa a Hukumar Ruwa ta Jihar Kano, inda ya samu gogewa a fannin aikin gwamnati. Har ila yau, ya taɓa riƙe muƙamin shugaban kwamitin gudanarwa na Cibiyar Shirye-shiryen Ilimi da Gudanarwa ta Ƙasa.

A siyasance, Abba Kabir Yusuf ya fara aikinsa a ƙarƙashin jagorancin tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, inda ya riƙe muƙamai daban-daban, ciki har da mataimaki na musamman da muƙamin sakatare na musamman da muƙamin babban sakatare, da kuma Kwamishinan ayyuka, gidaje da sufuri na Jihar Kano.

A shekarar 2018, ya tsaya takarar gwamna ƙarƙashin jam’iyyar PDP, wanda daga nan ne ma ya samo laƙabin sunan “Abba Gida-gida.” Duk da cewa bai yi nasara ba a wancan lokacin, amma bai karaya ba. A shekarar 2023, ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar NNPP tare da Jagoransa Sanata Kwankwaso, kuma ya lashe zaɓen gwamnan jihar.

Bayan lashe zaɓen, Abba Kabir Yusuf ya fuskanci ƙalubale na siyasa, ciki har da soke zaɓensa a kotun sauraron ƙararrakin zaɓe. Sai dai, ya ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ƙoli, inda aka tabbatar da zaɓensa a matsayin gwamnan jihar a watan Janairu 2024. Wannan ƙarfin hali da juriya da ya nuna sun ƙara masa daraja a matsayin shugaba wanda ba ya barin wani abu ya shagaltar da shi daga ƙoƙarin ciyar da jiharsa ta Kano gaba.

A wajen inganta rayuwar al’ummar Kano kuwa, Gwamna Yusuf yana gina sabbin gadoji a Ƙofar Dan Agundi da Tal’udu, domin rage cinkoson ababen hawa a jihar. Haka kuma, ya inganta fannin kiwon lafiya ta hanyar samar da kayan aiki da magunguna a asibitoci kyauta. Gwamnatinsa ta kuma ƙaddamar da shirin tallafa wa mata 5,200 da kuɗi Naira 50,000 a matsayin jari. Wannan tallafi na nufin taimaka wa mata wajen ƙarfafa wa kasuwancinsu da rage talauci a tsakaninsu.

Haka kuma, gwamnatinsa ta canza fitilun kan titunan Kano zuwa masu amfani da hasken rana, wanda ya sanya titunan jihar zama cikin haske ko yaushe tare da rage amfani da makamashi mara tsafta. Gwamna Yusuf yana biyan albashi, fansho, da kuɗin sallama akai-akai, kuma ya kasance cikin gwamnonin farko a Nijeriya da suka fara aiwatarwa da biyan mafi ƙarancin albashi na Naira 71,000. Bugu da ƙari, gwamnatinsa ta biya bashin Naira biliyan 3.5 na ƙasashen waje da Naira biliyan 60 na cikin gida, ta rage bashin jihar zuwa Naira biliyan 127.8 a tsakiyar shekarar 2024.

Alhaji Abba Kabir Yusuf ya zama jajirtaccen gwamna wanda ya yi fice wajen kawo sauyi a fannin ilimi da lafiya da gine-gine da kuma tallafa wa jama’a. Jagorancinsa ya zama abin misali a Nijeriya, burinsa bai wuce sanya murmushi a fuskar Kanawa ba.

Gwamna
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

MASU ALAKA

Bala Mohammed
Labarai

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa
Manyan Labarai

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara
Labarai

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Next Post
Gwarzon Ɗan Siyasar Shekarar 2024: Adams Oshiomhole (CON)

Gwarzon Ɗan Siyasar Shekarar 2024: Adams Oshiomhole (CON)

LABARAI MASU NASABA

Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.