• English
  • Business News
Friday, May 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

by Muhammad and Leadership Hausa
6 months ago
in Labarai
0
Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jagorancin Alhaji Bashir Adewale Adeniyi a matsayin Shugaban Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS), ya kawo sauye-sauye masu matuƙar tasiri, inda ya samar da zaman lafiya da inganta aiki da ƙaruwar kuɗaɗen shiga. Wannan nasara ta taimaka matuƙa wajen bunƙasar tattalin arziƙin Nijeriya, wanda ya sa aka zaɓe shi a matsayin Gwarzon Ma’aikaci Na Shekarar 2024.

Tun bayan naɗa shi muƙamin a watan Yunin 2023, Adeniyi ya fuskanci manyan matsaloli a hukumar, wanda suka haɗa da rashin ƙwarewar aiki da cin hanci da rashawa, da tsofaffin hanyoyin aiki. Ta hanyar amfani da hangen nesa da ƙwazo, ya bijiro da sababbin tsare-tsare a hukumar, wanda ya nuna yadda za a iya kawo gyare-gyare masu kyau a ɓangaren ayyukan gwamnati a Nijeriya.

  • Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters
  • Gwamnan Shekarar 2024: Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke

Dabarun Adeniyi sun fi mayar da hankali kan sauƙaƙa ayyukan Kwastam da kuma inganta kasuwanci.

Ɗaya daga cikin manyan sauye-sauyensa shi ne rage yawan tawagar da hukumar ke da su, inda ya haɗe rundunar Strike Force Teams da Federal Operations Unit (FOU). Wannan ya rage yawan shingen bincike daga biyar zuwa biyu a kowace hanya, wanda ya sauƙaƙa harkokin kasuwanci kuma ya rage cin hanci a kan iyaka. Wannan gyara ya ƙara wanzar da gaskiya a aikin hukumar tare da tallafa wa kasuwanci, inda ya kafa sabon mizanin inganta aiki.

A ƙarƙashin shugabancinsa, hukumar NCS ta ƙarfafa haɗin guiwar ƙasa da ƙasa, musamman da Ƙungiyar Kwastam ta Duniya (WCO), don tabbatar da amfani da kyawawan ƙa’idojin aiki na ƙasa da ƙasa. Adeniyi ya kuma mayar da hankali kan tsaro a iyakokin ƙasa ta hanyar samar da sabbin dabaru, kamar sayen jirgin sama ƙirar Cessna Grand Caravan EX-208B domin bincike ta sama. Wannan jirgin ya inganta aikin sintiri a wuraren da ke da wahalar zuwa, wanda ya bunƙasa yaƙi da safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Sabunta fasaha shi ma wani ginshiƙi ne a jagorancin Adeniyi. Ya jagoranci shirye-shirye irin su Authorized Economic Operators (AEO), wanda ya sauƙaƙa aikin Kwastam ga ‘yan kasuwa masu bin doka tare da ƙara musu damar yin gogayya a kasuwannin duniya.

Ƙaddamar da Time Release Study (TRS) da amfani da fasahar geospatial ya ƙara tabbatar da jajircewarsa wajen amfani da fasaha domin inganta aiki da samun sahihanci.

Waɗannan sauye-sauye sun haifar da sakamako mai tasirin gaske a fannin tattalin arziƙi. Kuɗaɗen shiga na wata-wata sun ƙaru da kashi 70.13, daga Naira biliyan 202 zuwa sama da Naira biliyan 343.

A shekarar 2023, duk da ragi da aka samu a harkokin kasuwanci, hukumar ta samu jimillar kuɗin shiga har Naira tiriliyan 3.2, wanda hakan ya ƙaru da kashi 21.4 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, wannan ya nuna cewa Adeniyi ya inganta kuɗaɗen gwamnati ta hanyar samar da tsari mai inganci.

Bugu da ƙari, Adeniyi ya ƙara ƙarfi a ɓangaren aiwatar da dokoki. A shekarar 2023 kaɗai, hukumar ta kama kayayyaki 1,763 da darajar kuɗinsu ta kai Naira biliyan 11.9 a matsayin kuɗin haraji, tare da gurfanar da mutane 52. Wannan tsauraran matakai sun ƙara tabbatar da sadaukarwarsa wajen kare tattalin arziƙin Nijeriya daga illolin safarar kayan haram.

Duk da waɗannan nasarori, Adeniyi ya ci gaba da duba yadda zai ƙara inganta harkokin kasuwanci. Burinsa na gaba ya haɗa da samar da sabbin dabarun aiki a iyakoki, gyara tsarin TRS da shirye-shiryen AEO, tare da rage jinkiri a harkokin gwamnati.

Haka kuma yana ƙoƙarin wayar da kan jama’a kan illolin da safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba ke yi wa tattalin arziƙi, tare da tabbatar da Nijeriya ta samu matsayi mai kyau a kasuwannin duniya.

Jagorancin Adeniyi ya zama misali a tsakanin shugabannin ma’aikatun gwamnati, wanda hakan ya sa ya cancanci wannan lambar yabo daga Jaridar Leadership


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiBashir Adewale Adeniyi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Rikicin Manoma Da Makiyaya A Nijeriya

Next Post

Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

Related

Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Labarai

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

2 hours ago
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

4 hours ago
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 
Manyan Labarai

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

5 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

INEC Ta Samar Da Sashen Ƙirƙirarriyar Basira Domin Inganta Harkokin Zaɓe 

7 hours ago
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ra'ayi Riga

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

8 hours ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

9 hours ago
Next Post
Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

May 22, 2025
Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

May 22, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

May 22, 2025
Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

May 22, 2025
Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

May 22, 2025
Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

May 22, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

May 22, 2025
Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

May 22, 2025
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

May 22, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

May 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.