• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

by Muhammad and Leadership Hausa
9 months ago
in Labarai
0
Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jagorancin Alhaji Bashir Adewale Adeniyi a matsayin Shugaban Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS), ya kawo sauye-sauye masu matuƙar tasiri, inda ya samar da zaman lafiya da inganta aiki da ƙaruwar kuɗaɗen shiga. Wannan nasara ta taimaka matuƙa wajen bunƙasar tattalin arziƙin Nijeriya, wanda ya sa aka zaɓe shi a matsayin Gwarzon Ma’aikaci Na Shekarar 2024.

Tun bayan naɗa shi muƙamin a watan Yunin 2023, Adeniyi ya fuskanci manyan matsaloli a hukumar, wanda suka haɗa da rashin ƙwarewar aiki da cin hanci da rashawa, da tsofaffin hanyoyin aiki. Ta hanyar amfani da hangen nesa da ƙwazo, ya bijiro da sababbin tsare-tsare a hukumar, wanda ya nuna yadda za a iya kawo gyare-gyare masu kyau a ɓangaren ayyukan gwamnati a Nijeriya.

  • Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters
  • Gwamnan Shekarar 2024: Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke

Dabarun Adeniyi sun fi mayar da hankali kan sauƙaƙa ayyukan Kwastam da kuma inganta kasuwanci.

Ɗaya daga cikin manyan sauye-sauyensa shi ne rage yawan tawagar da hukumar ke da su, inda ya haɗe rundunar Strike Force Teams da Federal Operations Unit (FOU). Wannan ya rage yawan shingen bincike daga biyar zuwa biyu a kowace hanya, wanda ya sauƙaƙa harkokin kasuwanci kuma ya rage cin hanci a kan iyaka. Wannan gyara ya ƙara wanzar da gaskiya a aikin hukumar tare da tallafa wa kasuwanci, inda ya kafa sabon mizanin inganta aiki.

A ƙarƙashin shugabancinsa, hukumar NCS ta ƙarfafa haɗin guiwar ƙasa da ƙasa, musamman da Ƙungiyar Kwastam ta Duniya (WCO), don tabbatar da amfani da kyawawan ƙa’idojin aiki na ƙasa da ƙasa. Adeniyi ya kuma mayar da hankali kan tsaro a iyakokin ƙasa ta hanyar samar da sabbin dabaru, kamar sayen jirgin sama ƙirar Cessna Grand Caravan EX-208B domin bincike ta sama. Wannan jirgin ya inganta aikin sintiri a wuraren da ke da wahalar zuwa, wanda ya bunƙasa yaƙi da safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba.

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

Sabunta fasaha shi ma wani ginshiƙi ne a jagorancin Adeniyi. Ya jagoranci shirye-shirye irin su Authorized Economic Operators (AEO), wanda ya sauƙaƙa aikin Kwastam ga ‘yan kasuwa masu bin doka tare da ƙara musu damar yin gogayya a kasuwannin duniya.

Ƙaddamar da Time Release Study (TRS) da amfani da fasahar geospatial ya ƙara tabbatar da jajircewarsa wajen amfani da fasaha domin inganta aiki da samun sahihanci.

Waɗannan sauye-sauye sun haifar da sakamako mai tasirin gaske a fannin tattalin arziƙi. Kuɗaɗen shiga na wata-wata sun ƙaru da kashi 70.13, daga Naira biliyan 202 zuwa sama da Naira biliyan 343.

A shekarar 2023, duk da ragi da aka samu a harkokin kasuwanci, hukumar ta samu jimillar kuɗin shiga har Naira tiriliyan 3.2, wanda hakan ya ƙaru da kashi 21.4 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, wannan ya nuna cewa Adeniyi ya inganta kuɗaɗen gwamnati ta hanyar samar da tsari mai inganci.

Bugu da ƙari, Adeniyi ya ƙara ƙarfi a ɓangaren aiwatar da dokoki. A shekarar 2023 kaɗai, hukumar ta kama kayayyaki 1,763 da darajar kuɗinsu ta kai Naira biliyan 11.9 a matsayin kuɗin haraji, tare da gurfanar da mutane 52. Wannan tsauraran matakai sun ƙara tabbatar da sadaukarwarsa wajen kare tattalin arziƙin Nijeriya daga illolin safarar kayan haram.

Duk da waɗannan nasarori, Adeniyi ya ci gaba da duba yadda zai ƙara inganta harkokin kasuwanci. Burinsa na gaba ya haɗa da samar da sabbin dabarun aiki a iyakoki, gyara tsarin TRS da shirye-shiryen AEO, tare da rage jinkiri a harkokin gwamnati.

Haka kuma yana ƙoƙarin wayar da kan jama’a kan illolin da safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba ke yi wa tattalin arziƙi, tare da tabbatar da Nijeriya ta samu matsayi mai kyau a kasuwannin duniya.

Jagorancin Adeniyi ya zama misali a tsakanin shugabannin ma’aikatun gwamnati, wanda hakan ya sa ya cancanci wannan lambar yabo daga Jaridar Leadership


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiBashir Adewale Adeniyi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Rikicin Manoma Da Makiyaya A Nijeriya

Next Post

Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

Related

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

4 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

5 hours ago
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu
Labarai

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

6 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

7 hours ago
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

7 hours ago
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
Labarai

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

7 hours ago
Next Post
Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.