ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Shekarar 2024: Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke

by Leadership Hausa
2 years ago
Ademola

Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke, wanda aka fi sani da “Gwamnan Mai Rawa”, ya samu lambar yabo ta LEADERSHIP ta Gwarzon Gwamnan Shekara saboda irin gudunmawar da ya bayar wajen kawo sauyi da yawa a Jihar Osun.

Jagorancinsa ya ƙunshi inganta ababen more rayuwa da samar da walwalar ma’aikata da tsofaffi da bunƙasa harkokin noma da tabbatar da ci gaba mai ɗorewa. Wannan karramawa ta nuna yadda jagorancinsa ke inganta rayuwar al’umma cikin gaskiya da aminci.

  • Gwarzon Ɗan Siyasar Shekarar 2024: Adams Oshiomhole (CON)
  • Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf

Tarihi da Karatunsa;

ADVERTISEMENT

An haifi Adeleke a Jihar Osun. Ya fara karatunskaratu a firamare ta Methodist da Nawarudeen, ya yi makarantar sakandare ta Ede Muslim Grammar School Ede, daga nan kuma ya ci gaba da karatunsa a Jami’ar Atlanta Metropolitan State College, inda ya samu digiri a ɓangaren shari’a kan manyan laifuka (Criminal Justice) a 2021. Daga ya ci gaba da ƙara zurfafa iliminsa.

Sanata Adeleke ya fara siyasarsa a 2017, lokacin da ya tsaya takarar Sanatan Osun ta Yamma bayan rasuwar ɗan uwansa, Sanata Isiaka Adetunji Adeleke. Duk da cewa a lokacin yana sabuwar fuska a harkar siyasa amma ya samu nasarar lashe kujerar, duk da kasancewar APC ce mai mulki a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

A 2018, ya zama ɗan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, inda ya sha gwagwarmayar shari’a kan takararsa. Duk da rasa nasara a kotun ƙoli, ya sake jajircewa da shiryawa don takarar gwamna a 2022, inda ya samu nasarar doke gwamna mai ci, Adegboyega Oyetola. Wannan ya tabbatar da karɓuwarsa a tsakanin jama’ar jihar.

Nasarori A Matsayin Gwamna;

Bayan hawa mulki, Adeleke ya mayar da hankali kan cika alƙawurran da ya ɗaukarwa al’ummarsa yayin yaƙin neman zaɓe. Ya fara kammala ayyukan da aka bari ba a ƙarasa ba, tare da ƙaddamar da sababbin ayyukan da suka shafi rayuwar jama’ar jihar kai-tsaye, kamar hanyoyi da gadaje da gina titunan a faɗin jihar. A cikin watanni 11 na farkon mulkinsa, Adeleke ya fara gadoji a Osogbo da Ile-Ife da Ilesa da kuma Ede. Ya ƙaddamar da tsarin Naira biliyan 100 don ci gabagaba da gudanar da manyan ayyuka ba tare da dogaro da cin bashi ba.

Gwamna Adeleke ya tabbatar da biyan albashi da fansho akan lokaci, yana cika alƙawarinsa na biyan albashin da aka bari bashi a baya. Wannan ya ja hankalin ma’aikatan Jihar Osun, inda suke masa laƙabi da “Mutum na mutane”.

Noma da Kiwo;

Adeleke ya mayar da hankali kan bunƙasa harkokin noma domin inganta samar da abinci da tattalin arziƙin jihar. Ya raba injinan noma da kayan aikin gona ga manoma, ya kuma ƙaddamar da tsarin Osun Broilers Outgrower, wanda ya bayar da tallafi ga masu kiwon Kaji.

A ɓangaren ilimi kuwa, Adeleke ya dawo da tallafin karatu ga ɗalibai a manyan makarantun jihar, ya kuma tabbatar da fara aikin Jami’ar Ilesa da kuma gyaran makarantu a faɗin jihar. Wannan ya ƙara wa yara damar samun ingantaccen ilimi a tsari mai kyau da tsaro.

A ɓangaren lafiya, ya gyara tare da gina sababbin cibiyoyin lafiya sama da 120 daga cikin 345 da ake shirin sabuntawa a jihar. Kazalika, ya gabatar da shirye-shiryen lafiya kyauta, ciki har da tiyatar ido, wanda ake gudanarwa a duk faɗin jihar don tallafa wa jama’a.

Tallafi ga Mata da Matasa

A ƙarƙashin shirin Opon Imo Empowerment, Gwamna Adeleke ya samar da tallafi da horo ga matasa da mata don kafa ƙananan sana’o’i. Wannan ya rage zaman kashe wando tare da ba su damar samun dogaro da kai.

Adeleke ya shahara da halin kula jama’arsa, inda yake sauraron ƙorafe-ƙorafensu tare da mayar da hankali kan ayyukan da za su amfani al’umma. Wannan salon jagoranci ya ƙara masa farin jini da karɓuwa a zuƙatan jama’a, inda ake ganinsa a matsayin jagoran da ke kula da al’ummarsa. Jagorancin Adeleke ya kawo sauyi a Jihar Osun, inda ya tabbatar da cewa kowanne ɓangare na rayuwar al’umarsa sun samu ci gaba.

Ademola
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
Manyan Labarai

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027
Manyan Labarai

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000
Labarai

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Next Post
Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters

Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.