ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Shekarar 2024: Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke

by Leadership Hausa
2 years ago
Ademola

Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke, wanda aka fi sani da “Gwamnan Mai Rawa”, ya samu lambar yabo ta LEADERSHIP ta Gwarzon Gwamnan Shekara saboda irin gudunmawar da ya bayar wajen kawo sauyi da yawa a Jihar Osun.

Jagorancinsa ya ƙunshi inganta ababen more rayuwa da samar da walwalar ma’aikata da tsofaffi da bunƙasa harkokin noma da tabbatar da ci gaba mai ɗorewa. Wannan karramawa ta nuna yadda jagorancinsa ke inganta rayuwar al’umma cikin gaskiya da aminci.

  • Gwarzon Ɗan Siyasar Shekarar 2024: Adams Oshiomhole (CON)
  • Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf

Tarihi da Karatunsa;

ADVERTISEMENT

An haifi Adeleke a Jihar Osun. Ya fara karatunskaratu a firamare ta Methodist da Nawarudeen, ya yi makarantar sakandare ta Ede Muslim Grammar School Ede, daga nan kuma ya ci gaba da karatunsa a Jami’ar Atlanta Metropolitan State College, inda ya samu digiri a ɓangaren shari’a kan manyan laifuka (Criminal Justice) a 2021. Daga ya ci gaba da ƙara zurfafa iliminsa.

Sanata Adeleke ya fara siyasarsa a 2017, lokacin da ya tsaya takarar Sanatan Osun ta Yamma bayan rasuwar ɗan uwansa, Sanata Isiaka Adetunji Adeleke. Duk da cewa a lokacin yana sabuwar fuska a harkar siyasa amma ya samu nasarar lashe kujerar, duk da kasancewar APC ce mai mulki a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

A 2018, ya zama ɗan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, inda ya sha gwagwarmayar shari’a kan takararsa. Duk da rasa nasara a kotun ƙoli, ya sake jajircewa da shiryawa don takarar gwamna a 2022, inda ya samu nasarar doke gwamna mai ci, Adegboyega Oyetola. Wannan ya tabbatar da karɓuwarsa a tsakanin jama’ar jihar.

Nasarori A Matsayin Gwamna;

Bayan hawa mulki, Adeleke ya mayar da hankali kan cika alƙawurran da ya ɗaukarwa al’ummarsa yayin yaƙin neman zaɓe. Ya fara kammala ayyukan da aka bari ba a ƙarasa ba, tare da ƙaddamar da sababbin ayyukan da suka shafi rayuwar jama’ar jihar kai-tsaye, kamar hanyoyi da gadaje da gina titunan a faɗin jihar. A cikin watanni 11 na farkon mulkinsa, Adeleke ya fara gadoji a Osogbo da Ile-Ife da Ilesa da kuma Ede. Ya ƙaddamar da tsarin Naira biliyan 100 don ci gabagaba da gudanar da manyan ayyuka ba tare da dogaro da cin bashi ba.

Gwamna Adeleke ya tabbatar da biyan albashi da fansho akan lokaci, yana cika alƙawarinsa na biyan albashin da aka bari bashi a baya. Wannan ya ja hankalin ma’aikatan Jihar Osun, inda suke masa laƙabi da “Mutum na mutane”.

Noma da Kiwo;

Adeleke ya mayar da hankali kan bunƙasa harkokin noma domin inganta samar da abinci da tattalin arziƙin jihar. Ya raba injinan noma da kayan aikin gona ga manoma, ya kuma ƙaddamar da tsarin Osun Broilers Outgrower, wanda ya bayar da tallafi ga masu kiwon Kaji.

A ɓangaren ilimi kuwa, Adeleke ya dawo da tallafin karatu ga ɗalibai a manyan makarantun jihar, ya kuma tabbatar da fara aikin Jami’ar Ilesa da kuma gyaran makarantu a faɗin jihar. Wannan ya ƙara wa yara damar samun ingantaccen ilimi a tsari mai kyau da tsaro.

A ɓangaren lafiya, ya gyara tare da gina sababbin cibiyoyin lafiya sama da 120 daga cikin 345 da ake shirin sabuntawa a jihar. Kazalika, ya gabatar da shirye-shiryen lafiya kyauta, ciki har da tiyatar ido, wanda ake gudanarwa a duk faɗin jihar don tallafa wa jama’a.

Tallafi ga Mata da Matasa

A ƙarƙashin shirin Opon Imo Empowerment, Gwamna Adeleke ya samar da tallafi da horo ga matasa da mata don kafa ƙananan sana’o’i. Wannan ya rage zaman kashe wando tare da ba su damar samun dogaro da kai.

Adeleke ya shahara da halin kula jama’arsa, inda yake sauraron ƙorafe-ƙorafensu tare da mayar da hankali kan ayyukan da za su amfani al’umma. Wannan salon jagoranci ya ƙara masa farin jini da karɓuwa a zuƙatan jama’a, inda ake ganinsa a matsayin jagoran da ke kula da al’ummarsa. Jagorancin Adeleke ya kawo sauyi a Jihar Osun, inda ya tabbatar da cewa kowanne ɓangare na rayuwar al’umarsa sun samu ci gaba.

Ademola
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati
Labarai

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare
Labarai

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Next Post
Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters

Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.