• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Shekarar 2024: Barr. Nyesom Ezenwo Wike

by Leadership Hausa
7 months ago
in Labarai
0
Gwarzon Shekarar 2024: Barr. Nyesom Ezenwo Wike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Barrister Nyesom Ezenwo Wike, wanda aka fi sani da “Mr. Project”, ya samu lambar yabo ta Jaridar LEADERSHIP saboda irin gudummawarsa wajen samar da ci gaba ta hanyar samar da ababen more rayuwa ga al’umma a yankunan karkara da birane.

A matsayinsa na ministan babban birnin tarayya, ya kawo sauye-sauye masu yawa, wanda hakan ya sa ya zama jagora mai hangen nesa da jajircewa.

  • Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf
  • Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

Tarihi da Karatunsa

An haifi Wike a garin Rumuepirikom, Obio-Akpor da ke Jihar Ribas, a ranar 13 ga Disamba, 1967. Ya karatu a sakandaren gwamnati a Eneka, daga nan ya shiga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Ribas (RSUST), inda ya samu digiri na farko a fannin Shari’a (Law). Bayan haka, ya halarci makarantar koyon aikin lauya (Law School) a shekarar 1997, kuma daga bisani ya samu digiri na biyu a Siyasa da tsare-tsare (Political and Administrative Studies) daga wannan jami’a.

Shigarsa Siyasa

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Wike ya shiga harkokin siyasa a 1999, lokacin da ya zama shugaban ƙaramar hukumar Obio-Akpor, wanda ya yi shekaru takwas yana mulki. Daga bisani ya zama Shugaban ma’aikata na gwamna Rotimi Amaechi. A shekarar 2011, an naɗa shi ƙaramin Ministan Ilimi a ƙarƙashin gwamnatin Goodluck Jonathan, inda ya kai matsayin Ministan Ilimi mai cikakken iko a 2013.

A matsayinsa na minista, ya kawo sauye-sauye masu mahimmanci a tsarin ilimi a Nijeriya. Ya kuma jagoranci sauyin manufofin da suka inganta damar samun ingantaccen ilimi a duk faɗin Nijeriya.

Gwamnan Jihar Ribas

A ranar 29 ga Mayu, 2015, Wike ya zama Gwamnan Jihar Ribas, inda ya gudanar da ayyukan ci gaba masu tarin yawa. A cikin shekaru takwas na mulkinsa, ya gabatar da ayyukan gine-gine da samar da hanyoyi da inganta lafiya da kuma haɓaka ilimi. Ya kuma tabbatar da biyan albashin ma’aikata akan lokaci da biyan kuɗaɗen ‘yan fansho da tsofaffin ma’aikata. Ya ƙaddamar da ayyukan da suka shafi rayuwar mutanen jiharsa masu muhimmanci, ciki har da samar da hanyoyin mota da gadaje da titunan a birane da karkara. Wannan ya sauya fuskar Jihar Ribas, hakan ya sa al’umma suka amince da jagorancinsa.

Matsayin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT)

An naɗa Wike a matsayin ministan babban birnin tarayya (FCT) a ranar 16 ga Agusta, 2023. Da hawansa wannan matsayi, ya yi duba na musamman kan ayyukan da aka fara amma ba a kammala ba a Abuja. Ya gano manyan matsaloli, musamman waɗanda suka shafi rashin isassun kuɗaɗe, sannan ya ɗauki matakan gaggawa don magance su.

A matsayinsa na minista, Wike ya tabbatar da shugabanci mai kyau wajen bayar da kwangiloli, yana mai cewa ba zai bayar da kwangila ba, ba tare da an tabbatar da kuɗin da ake da su ba a ƙasa ba. Wannan ya kawo gaskiya da inganci a tsarin gudanarwa. Ya gina hanyoyi,

da asibitoci da makarantu a sassa daban-daban na Abuja, ya kuma tabbatar da cewa kowanne yanki ya amfana da shugabancinsa.

Haka kuma, ya sake farfaɗo da filin jirgin saman Abuja na biyu, wanda ya kawo sauƙi ga zirga-zirgar jiragen sama. Ya kuma samar da ingantaccen tsarin sufuri wanda ya rage cunkoso da bunƙasa kasuwanci a Abuja.

Walwalar Ma’aikata da Aikace-aikace

A ƙarƙashin jagorancinsa, Wike ya tabbatar da biyan albashin malaman makaranta da sauran ma’aikata da ya gada a matsayin bashi. Har ila yau, ya inganta walwalar ma’aikata ta hanyar ƙarawa sama da 1,000 girma, wanda hakan ya ƙara musu kwarin gwuiwa. Wike ya tabbatar da cewa ya bai wa sha’anin tsaro fifiko, inda ya haɗa kai da hukumomin tsaro da ƙungiyoyin sa kai don tabbatar da zaman lafiya a Abuja. Wannan ya rage yawan laifuka a birnin, kuma ya ƙara ƙwarin gwuiwar jama’a kan aikin hukumomin tsaro.

Salon Jagorancinsa

Kowa ya san Minista Wike, gwani ne wajen bai wa jama’a kula. Yana ziyartar wuraren gudanar da ayyuka, yana sauraron ƙorafe-ƙorafen jama’a, sannan yana tabbatar da cewa an magance matsalolin da suka taso cikin ƙanƙanin lokaci. Wannan salon jagoranci ya sa jama’a suka gamsu da da irin shugabancinsa.

A yau, Minista Wike ya kafa tarihi a babban birnin tarayya ta fuskar aiyukansa na bunƙasa hanyoyin more rayuwa da walwalar jama’a da tsaro, wanda hakan ya tabbatar da cewa yana da hangen nesa da jajircewa wajen bunƙasa Abuja. Wannan lambar yabo tana nuna yadda ya ke amfani da jagorancinsa wajen kawo ci gaba mai ma’ana ga jama’arsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Shekarar 2024: Mallam Umar A. Namadi

Next Post

Hukumar Gwamnati Mafi Ƙwazo A Shekarar 2024: Hukumar Ilimin Bai-ɗaya (UBEC)

Related

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

19 minutes ago
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
Labarai

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

2 hours ago
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027
Labarai

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

4 hours ago
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta
Labarai

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

4 hours ago
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

6 hours ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

7 hours ago
Next Post
UBEC

Hukumar Gwamnati Mafi Ƙwazo A Shekarar 2024: Hukumar Ilimin Bai-ɗaya (UBEC)

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.