• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Kula Da Ilimin Almajirai Da Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta Za Ta Saka Yara Miliyan 10 A Makarantu

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
Almajirai

Yayin da musulmai suka yi bikin Babbar Sallah, hukumar kula da ilimin Almajirai da yaran da ba sa zuwa makaranta, ta kara jaddada aniyarta ta daukar nauyin yara miliyan 10 da ba sa zuwa makaranta daga nan zuwa shekara ta 2027.

Babban Sakatare kuma Shugaban Hukumar; Dakta Muhammad Sani Idris, shi ne ya bayyana haka a sakonsa na barka da Sallah a ranar Lahadin da ta gabata, sannan ya jinjina wa kokarin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, na taimaka wa yara wadanda ba sa zuwa makaranta, inda ya kara jaddada mayar da hankali a kan lamarin ilimin yaran.

  • Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja
  • Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Kamar yadda ya ce, hukumar na matukar yin kokari yadda ya kamata; wajen kula tare da koyar da almajirai ilimi, inda ya kara jaddada aniyar tasu ta samar da tsarin ilimi mai nagarta, wanda zai bai wa yaran da ba sa zuwa makaranta damar samun kyakkyawar rayuwa a nan gaba.

Shugaban ya kara da cewa, “Ina isar da gaisuwata ga dukkanin al’ummar Nijeriya, wadanda suke yi mana fata na musamman; dangane da wannan daukar nauyi da wannan hukuma ke yi dangane abubuwan da suka shafi ilimin almajirai da yara kanana, wadanda ba sa zuwa makaranta.

“Ina yin kira ga masu ruwa da tsaki, da su kara mayar da hankali tare da himmatuwa a kan wannan lamari da ya shafi ilimi. Domin kuwa, ta hanyar ilimi ne kadai ake iya bai wa matasa dama, inda za su nuna kwazonsu domin a taimaka masu su kasance wadanda za su taimakawa al’umma a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

“Ina mai nuna farincikina, a kan irin niyyar da Tinubu yake da ita na kawar da matsalolin da almajirai da yara kanana wadanda ba sa zuwa makaranta ke fuskanta a Nijeriya. Kulawar da yake nunawa a kan lamarin ilimi da ci gaban al’umma, hakan yana kara nuna wa ‘yan Nijeriya yadda gwamnatinsa ta mayar da hankali ga jin dadin ‘yan Nijeriya, musamman ma wadanda suke da bukatar a taimaka musu.

Bugu da kari ya ce, “Muna yin kokari wajen ganin sa lamarin ilimin Boko a cikin tsarin yadda za a koyar da wadannan almajira ,domin su ma su samu kyakkyawar rayuwa.

“Za kuma mu ci gaba da tuntuba da kuma yin hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki, wadanda suka hada da ma’aikatar ilimi ta tarayya da masu taimaka wa ci gaban ilimi, jihohi da kananan hukumomi, da su yi kokari wajen taimakawa dangane da matsalolin da suke addabar wadannan yara.

“Tsarin shugabanci na Shugaban Kasa Tinubu, na matukar taimakawa wajen cimma muradun; musamman ta yadda aka faro. Sannan, muna da tabbacin za mu tabbatar da sai kowane yaro ya kai ga samun hanyar samun ilimi mai nagarta ba tare da la’akari da yadda suka taso ko matsalolin da suke fuskanta ba”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
Ilimi

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
Next Post
Sabulu Na Musamman Domin Gyaran Fata Da Hadin Dilka

Sabulu Na Musamman Domin Gyaran Fata Da Hadin Dilka

LABARAI MASU NASABA

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.