• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Illar Amfani Da Manhajar VPN Ta Kyauta

by Ibrahim Sabo
3 years ago
in Rahotonni
0
Illar Amfani Da Manhajar VPN Ta Kyauta

Manhajar VPN

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manhajar Free VPN, wata manhaja ce da yake ba da damar yin dukkan nau’i na browsing a kyauta, amma yana da illoli matuka ga wayoyi da kuma rashin sirri ga mutum.

 Yin amfani da manhajar VPN na kyauta yana da matukar hadari, zai iya iya janyo wa mutum abin da ko da wasa baya taba tunaninsa.

  • Ba Mu Taba Ganin Ambaliyar Ruwa Mafi Muni A Nijeriya Kamar Ta Bana Ba – Gwamnati
  • Sin Tana Maraba Da Kiran Taron Sulhu Tsakanin Al’ummomin Libya

Gara ma wanda ake biya kafin amfani da su din, domin shi din ana iya kare bayanan sirri na mai amfani da shi a kan kudin da bai taka kara ya karya ba.

Akwai mutane da dama wadanda suke jin dadin amfani da manhajar VPN na kyauta, to ya kamata tun wuri su sani cewa, amfani da VPN yana tattare da illoli, ga su a kasa zamu yi bayani daya bayan daya.

Za A Iya Satar Bayananka

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Yawancin masu amfani da VPN ba su da masaniyar za a iya satar bayanansu cikin sauki. Daya daga cikin muhimman dalilan amfani da manhajar VPN shi ne ganin an kare ka daga masu kutse, to amma fargabar ita ce maganar gaskiya wasu manhajojin na VPN na kunshe da wani siddabaru da ake amfani da shi wajen satar bayanan kada kuma amfani da wannan dama wajen aiwatar da wata mummunar manufa da ake son cimmawa.

Irin wadannan manhajoji na kyauta na VPN na amfani da tallukan da suke sanyawa masu amfani da su wajen wawashe bayanansu, kasancewar sun dogara ne da ‘yan tallukan da suke samu wajen samun kudin shiga.

Bibiyar Duk Abin Da Kake Yi

Wasu suna amfani da manhajar VPN ne, saboda kare sirrinsu a lokacin da suke bincike a Internet ba, to sai dai yawancin manhajojin VPN na kyauta na da wasu mutane da aka sanya da ke bibiyar abubuwan da ke faruwa a cikinsu, suna tattara bayanan masu amfani da su, don haka a wannan bigire maimakon a aiko maka da wani tsari da kake da damar amincewa da shi ko ka latsa kalmar a’a, sai kawai a tunkudo maka talla, wanda a lokacin da kake kallonsa sai kuma a rikakwasar bayananka salin alin ba tare da ka danna komai ba.

Takaita Samun Bayanai

Yawancin VPN na kyauta na takaita adadin bayanan da za ka iya amfani da su. Suna yin wannan ne don tura masu amfani da su zuwa tsarin da ake biyan kudi kafin a samu cikakkiyar damar yin abin da ake sona yi, kamar yadda Hausawa ke cewa ”Iya kudinka iya shagalinka”

Manhajar VPN na haifar da damuwa ga masu amfani da ita saboda yadda take jinkirta sadarwar Intanet (rashin sauri).

Manhajar VPN na kyauta na haifar da jinkiri wajen samun bayanai a Intanet, abin da ke kawo damuwa ga wanda ke amfani da su, to dalilin shi ne yawancin mutane na raja’a ne ga na kyauta don cin bulus.

Sannan su kan su tallukan da suke sanyawa da zummar satar bayanai na iya haifar da rashin saurin na Intanet, dalilin sanya tallan shi ne tun da masu amfani da su garabasa kawai suke ci, to bari su tallata wata haja tun da dama masu karin maganasun ce” Da ruwan ciki ake jan na Rijiya”.

Barazanar Harbuwa Da Cututtukan Intanet

Manhajojin da ake amfani da su wajen sadarwa a waya ko na’urar kwamfuta ko kuma Intanet na dauke da wasu hanyoyi da yawa da ake sanya wa a cikinsu wajen satar bayanai ko yin kutse ko shirya wani siddabaru.

Wasu manhajojin na VPN da ake amfani da su a kyauta ana tsara su ne da zummar cewa masu su suna da ikon sarrafa bayanan mutane yadda suka ga dama, kuma suna ba da wannan ikon ga abokan cinikinsu masu biyan kudi don riba.

Wannan yana da matukar hadari kamar yadda ma su aikata laifuka ta yanar gizo ke iya yin amfani da wannan yanayin don kaddamar da hare-hare kan masu amfanida VPN da ba su da masaniyar duk wannan al’amari.

Manhajojin VPN na tattare da sarkakiya iri-iri da ke da bukatar zuba kudi da yawa a harkar don samar da kariya da kuma tsare bayanan ma su amfani da su.

Akwai kuma bukatar masu su, su rika sabunta tsare-tsaren ba da kariyar da suke amfani da su akai-akai daidai da zamani domin tabbatar da kare abokan huldarsu.

Sai dai kash, rashin mayar da hankali ga wadannan abubuwa da suka kamata ne ya sa masu manhajar VPN ta kyauta ke cin karensu babu babbaka ta hanyar cusa talluka da wasu tsare-tsare da ke zama babban hadari ga masu amfani da manhajar.

A kashin gaskiya, wannan ba wai kawai abu ne mai matukar hadari ba, ya kuma ci karo da dokokin bayar da kariya da tsaro da su kansu ka’idojin amfani da manhajojin na VPN.

Amfani da manhajar VPN zai zama ba kada cikakkiyar kariya a dukkan mu’amalarka ta Intanet.

Wasu kasashen tuni sun haramta amfani da manhajar VPN, saboda hadarin da ke tattare da ita. Dukkan sirrikanka suna hanun VPN muddin kana amfani da manhajar VPN.

Sannan amfanida manhajar VPN yana zukar data fiye da data ta asali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IllaManhajaSatar BayanaiVPN
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zamanintarwa Irin Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Shimfida Zaman lafiya Da Kwanciyar Hankalin Duniya

Next Post

Kasar Sin Kyakkyawa Za Ta Kara Samar Da Gudummawarta Ga Duniya

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Kasar Sin Kyakkyawa Za Ta Kara Samar Da Gudummawarta Ga Duniya

Kasar Sin Kyakkyawa Za Ta Kara Samar Da Gudummawarta Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.