• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Fatan Allah Ya Dauki Rayuwata A Dakin Mijina -Tsohuwar Jaruma Fati Ladan

by Sulaiman and Rabilu Sani Bena
2 years ago
in Nishadi
0
Fati Ladan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohuwar jaruma a masana’antar Kannywood, Hajiya Fati Ladan, ta bayyana dalilin da ya sa take har yanzu a gidan mijinta duk da cewar ana cewa ‘yan fim ba su cika zaman aure ba, kuma ta yi fatan Allah ya kashe ta a dakin mijinta.

Fati ta yi wadannan kalaman ne a hirar da ta yi da manema labarai dangane da cikar ta shekara goma cur a gidan aure a gidan mijin ta a Kaduna.

  • Kamfanonin Jirage Za Su Fara Biyan Tarar Jinkirta Tashi Da Soke Tafiya
  • Tinubu Ya Zama Gwarzon Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP

Alhaji Yerima Shettima, shugaban Kungiyar Tuntuba ta Matasan Arewa (Arewa Youth Consultatibe Forum), shi ne mijin ta.

Fati da Yerima dai su na da ‘ya’ya biyu a tsakanin su, A’isha Humaira da Muhammad Shafi’u, kuma su na zaune ne a Kaduna. Fati ita ce amarya a cikin matan sa biyu.

Da take amsa tambayoyin yan jarida Fati ta bayyana matukar godiyarta ga Allah (S.W.T.) da ya nuna mata wannan lokaci inda ta bayyana shekara goma ba kwana goma ba ne.
Ta kara da cewar zaman aurenta na tsawon shekaru 10 ba wani sirri ba ne illa kawai hakuri da soyayya saboda soyayya idan babu hakuri, sai ka ga kuma ba za a kai ga cimma inda ake so a kai ba.

Labarai Masu Nasaba

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Saboda a duk lokacin da mutum ya ce zai yi abu, musamman aure, to ina tunanin ba wasa ya je yi ba, aure abu ne wanda in har ka yanke hukuncin cewa za ka yi shi, ka san da sanin cewa ibada za ka je ka yi ba sharholiya ba.
A lokacin da na yanke shawarar zan je in yi aure, na sanya wa zuciya ta cewa zan je in zauna, ibada zan yi wannan abin da na sa wa rayuwa ta ya sa ban fuskanci wani kalubale dangane da zaman aure na ba ko in ji ina kewar wani abu ba.

Kuma miji na ya na ba ni goyon baya dari bisa dari a dukkan abin da na ce zan yi in dai bai saba wa addini na ba da al’ada ta zai ba ni goyon baya.
Hakan ne ya sa na maida shi kamar aboki a wuri na, shi kuma ya maida ni kawa a wurin shi duk abin da za mu yi, mu na yin shi tare da ni da shi ban yi ‘missing’ din wani abu ba, gaskiya, saboda duk abin da na ke nema ina samu a wurin miji na.

Da take amsa tambaya akan ko tana alfahari da kasancewarta tsohuwar jarumar fina finan Hausa, Fati Ladan ta ce a duk lokacin da na wuce har yanzu, za ka ji ana cewa,ba ku gane ta ba, ai ita ce Fati Ladan, tsohuwar jarumar nan,wasu da dama za su zo su yi hotuna da ni, kuma na san cewa in ba albarkacin fim ba, babu yadda za a yi a san ni to ina alfahari da wannan kwarai da gaske.

Kamar yadda aka yi mana kudin goro, aka ce ba mu zaman aure, ba haka ba ne. ni a tunani na ba auren ‘yan fim kadai ke mutuwa ba, amma da yake mu an san mu, dole za a rika yi mana kudin goro ana cewa ba mu zaman aure, amma mu na zaman aure.

Fati ta kuma bayyana cewar a halin yanzu ba ta sha’awar harkar fim “amma maganar in ji ina sha’awar harkar fim, ba na yi gaskiya,daga lokacin da na ce na hakura, na yi ritaya na aje, ko kuma na ba shi baya, ba wai don ba shi da wani abu ba aure na fuskanta, kuma ina fata Allah ya kashe ni a dakin miji na, shi ne fata na.

Daga karshe Fati Ladan ta bayyana cewa tana yiwa masoyanta fatan Alheri kuma tana mika sakon godiya ta musamman a kan soyayya da su ke nuna mata a lokacin da ta ke waje da kuma yanzu da tayi aure.

A ranar 20 ga Disamba, 2023 in Allah ya kai mu Fati Ladan da mijin ta Yerima Shettima za su cika shekara goma cur da aure an daura auren su ne a ranar Juma’a, 20 ga Disamba, 2013 a kofar gidan su Fati da ke Unguwar Sarki, Kaduna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: fati ladanKannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayern Munich: Me Yake Faruwa Da Zakarun Jamus A Bana?

Next Post

Mijina Na Fifita Ni A Kan Kishiyata, Ko Muna Shiga Hakkinta?

Related

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

3 days ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

4 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

1 week ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

2 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

4 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 month ago
Next Post
Mijina Na Fifita Ni A Kan Kishiyata, Ko Muna Shiga Hakkinta?

Mijina Na Fifita Ni A Kan Kishiyata, Ko Muna Shiga Hakkinta?

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.