ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Fatan Allah Ya Dauki Rayuwata A Dakin Mijina -Tsohuwar Jaruma Fati Ladan

by Sulaiman and Rabilu Sani Bena
3 years ago
Fati Ladan

Tsohuwar jaruma a masana’antar Kannywood, Hajiya Fati Ladan, ta bayyana dalilin da ya sa take har yanzu a gidan mijinta duk da cewar ana cewa ‘yan fim ba su cika zaman aure ba, kuma ta yi fatan Allah ya kashe ta a dakin mijinta.

Fati ta yi wadannan kalaman ne a hirar da ta yi da manema labarai dangane da cikar ta shekara goma cur a gidan aure a gidan mijin ta a Kaduna.

  • Kamfanonin Jirage Za Su Fara Biyan Tarar Jinkirta Tashi Da Soke Tafiya
  • Tinubu Ya Zama Gwarzon Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP

Alhaji Yerima Shettima, shugaban Kungiyar Tuntuba ta Matasan Arewa (Arewa Youth Consultatibe Forum), shi ne mijin ta.

ADVERTISEMENT

Fati da Yerima dai su na da ‘ya’ya biyu a tsakanin su, A’isha Humaira da Muhammad Shafi’u, kuma su na zaune ne a Kaduna. Fati ita ce amarya a cikin matan sa biyu.

Da take amsa tambayoyin yan jarida Fati ta bayyana matukar godiyarta ga Allah (S.W.T.) da ya nuna mata wannan lokaci inda ta bayyana shekara goma ba kwana goma ba ne.
Ta kara da cewar zaman aurenta na tsawon shekaru 10 ba wani sirri ba ne illa kawai hakuri da soyayya saboda soyayya idan babu hakuri, sai ka ga kuma ba za a kai ga cimma inda ake so a kai ba.

LABARAI MASU NASABA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Saboda a duk lokacin da mutum ya ce zai yi abu, musamman aure, to ina tunanin ba wasa ya je yi ba, aure abu ne wanda in har ka yanke hukuncin cewa za ka yi shi, ka san da sanin cewa ibada za ka je ka yi ba sharholiya ba.
A lokacin da na yanke shawarar zan je in yi aure, na sanya wa zuciya ta cewa zan je in zauna, ibada zan yi wannan abin da na sa wa rayuwa ta ya sa ban fuskanci wani kalubale dangane da zaman aure na ba ko in ji ina kewar wani abu ba.

Kuma miji na ya na ba ni goyon baya dari bisa dari a dukkan abin da na ce zan yi in dai bai saba wa addini na ba da al’ada ta zai ba ni goyon baya.
Hakan ne ya sa na maida shi kamar aboki a wuri na, shi kuma ya maida ni kawa a wurin shi duk abin da za mu yi, mu na yin shi tare da ni da shi ban yi ‘missing’ din wani abu ba, gaskiya, saboda duk abin da na ke nema ina samu a wurin miji na.

Da take amsa tambaya akan ko tana alfahari da kasancewarta tsohuwar jarumar fina finan Hausa, Fati Ladan ta ce a duk lokacin da na wuce har yanzu, za ka ji ana cewa,ba ku gane ta ba, ai ita ce Fati Ladan, tsohuwar jarumar nan,wasu da dama za su zo su yi hotuna da ni, kuma na san cewa in ba albarkacin fim ba, babu yadda za a yi a san ni to ina alfahari da wannan kwarai da gaske.

Kamar yadda aka yi mana kudin goro, aka ce ba mu zaman aure, ba haka ba ne. ni a tunani na ba auren ‘yan fim kadai ke mutuwa ba, amma da yake mu an san mu, dole za a rika yi mana kudin goro ana cewa ba mu zaman aure, amma mu na zaman aure.

Fati ta kuma bayyana cewar a halin yanzu ba ta sha’awar harkar fim “amma maganar in ji ina sha’awar harkar fim, ba na yi gaskiya,daga lokacin da na ce na hakura, na yi ritaya na aje, ko kuma na ba shi baya, ba wai don ba shi da wani abu ba aure na fuskanta, kuma ina fata Allah ya kashe ni a dakin miji na, shi ne fata na.

Daga karshe Fati Ladan ta bayyana cewa tana yiwa masoyanta fatan Alheri kuma tana mika sakon godiya ta musamman a kan soyayya da su ke nuna mata a lokacin da ta ke waje da kuma yanzu da tayi aure.

A ranar 20 ga Disamba, 2023 in Allah ya kai mu Fati Ladan da mijin ta Yerima Shettima za su cika shekara goma cur da aure an daura auren su ne a ranar Juma’a, 20 ga Disamba, 2013 a kofar gidan su Fati da ke Unguwar Sarki, Kaduna.

fati ladan
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
fati ladan
Rabilu Sani Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sani Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sani-bena/
    Bayelsa United Ta Lallasa Kano Pillars 4-1 A Yenagoa
  • Rabilu Sani Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sani-bena/
    Samson Adamu Na Nijeriya Ya Zama Sabon Sakatare Janar Na CAF
  • Rabilu Sani Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sani-bena/
    Neymar Na Duba Yiwuwar Ritaya Daga Ƙwallon Ƙafa A Ƙarshen Shekara
  • Rabilu Sani Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sani-bena/
    Jerin Sharuddan Da Chelle Ya Gindayawa NFF Domin Cigaba Da Jagorantar Super Eagles 

MASU ALAKA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Next Post
Mijina Na Fifita Ni A Kan Kishiyata, Ko Muna Shiga Hakkinta?

Mijina Na Fifita Ni A Kan Kishiyata, Ko Muna Shiga Hakkinta?

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.