• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Yi Wa Jam’iyyun Siyasa Gori A Kan Rajistar Mambobi

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Labarai, Siyasa
0
INEC Ta Yi Wa  Jam’iyyun  Siyasa Gori A  Kan Rajistar  Mambobi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zave mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa babu wata jam’iyyar siyasa a Nijeriya da ta kammala yi wa mambobinta rajista. Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu shi ya bayyana hakan lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a garin Benin.

Yakubu ya kalubalanci jam’iyyun siyasa su kammala yi wa mambobinsu rajista idan har suna so hukumar ta yi musu dukkan abun da suke bukata. Ya ce INEC ta fi su yawan mutane, wanda take da yawan masu rajistar zave da suka miliyan 93, kuma duk sun kamala rajistarsu. Ya ce, “Kamar yadda a yau INEC ke da mafi girman bayanai na ‘yan Nijeriya da suka kai miliyan 93, wadanda suka kamala yin rajistar zave.

  • INEC Ta Dakatar Da Sake Zabe A Kano, Enugu, Akwa Ibom Sakamakon Ayyukan ‘Yan Daba
  • Baya Ta Haihu: INEC Ta Rushe Babban Taron Jam’iyyar LP Na Kasa

Har yanzu muna jiran jam’iyyun siyasa su ba mu cikakkun bayanan rajistar mambobinsu ko da a unguwa daya ne. “Babu wata jam’iyyar siyasa da ke da cikakken rajistar mambobinta ko da a unguwa daya. Amma idan sun zo taro irin wannan, za su rika kiranmu mu yi

musu abubuwan da suke bukata. “Wata gudunmawa kuka bayar matsayinku na jam’iyyan siyasa domin inganta tsarin dimokuradiyyarmu? Idan akwai jam’iyyar da ke da cikakken rajistar mambobinta a Jihar Edo ta daga hannu. Sannan zan kawo bayanan da kuka mika wa INEC in tabbatar da cewa ba gaskiya suke fadi ba. “Akwai lokacin da muka ce a kawo muna duk bayanan Abuja.

Sai wasu jam’iyyu suka fara cewa muna kai bayanan rajista daga unguwa zuwa Abuja yana da wuya. Amma ba gaskiya ba ne, saboda ba su kamala ba.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Yakubu ya kara da cewa ana ci gaba da yin rajistar masu zave don bai wa wadanda ba su da katin zave damar yin rajistar zave da wadanda nasu ya vace da kuma wadanda suke bukatar sauya wurin yin zave.

Yayin da yake nuna rashin amincewa da ikirari da ake yi na cewa matasan sun rasa kwarin gwiwa daga wurin hukumar sakamakon zaven 2023 da aka gudanar, ya bayyana cewa mafi yawan wadanda a halin yanzu ke yin rajistar zave a jihohin Edo da Ondo matasa ne wanda shekarunsu yake tsakanin 18 zuwa 34. Ya ce lallai bai yarda matasa sun rasa kwarin kwiwa ga hukumar zave ba, domin suke yin tururuwan yin rajistar zave.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Falalar Goman Farko Na Watan Fahimtar Sayyidina Umar (RA) Da Sayyidina Aliyu (RA) Kan Ramakon Ramadan A Goman Zulhajji

Next Post

Wasu Hakkokin Miji Da Suka Kamata Mata Su Mayar Da Hankali A Kai

Related

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi
Labarai

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

1 hour ago
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
Manyan Labarai

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

3 hours ago
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina
Labarai

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

12 hours ago
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi
Labarai

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

13 hours ago
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21
Labarai

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

15 hours ago
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC
Siyasa

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

16 hours ago
Next Post
Wasu Hakkokin Miji Da Suka Kamata  Mata Su Mayar Da Hankali A Kai

Wasu Hakkokin Miji Da Suka Kamata Mata Su Mayar Da Hankali A Kai

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.