ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an APC 3 A Jihar Zamfara Da Aka Dakatar Sun Maka Jam’iyyar A Kotu

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
4 weeks ago
APC

Jami’ai uku da aka dakatar na jam’iyyar APC a karamar hukumar Shinkafi ta Jihar Zamfara sun shigar da jam’iyyar kara a gaban kotu suna kalubalantar dakatarwa da aka yi musu a matsayin rashin bin dokar jam’iyyar.

 

Babangida Aliyu Shinkafi da Kabiru Ibrahim da kuma Ibrahim D. Kurya sun shigar da kara a gaban babban kotun Jihar Zamfara da ke Gusau, a ranar 14 ga Nuwamba, 2025, suna nemi kotu ta soke dakatarwar da aka yi musu da kuma hana ci gaba da kamfe na tsoratarwa da cin zarafi da nuna wariya daga shugabancin jam’iyyar a jihar. Cikin wadanda ake karar sun hada da jam’iyyar APC, Alhaji Tukur DanFulani Maikatako da Alhaji Ibrahim Bama Shinkafi.

ADVERTISEMENT

 

Mambobin jam’iyyar uku, wadanda suke aiki a matsayin shugaban gunduma, sakataren walwala da wakilin masu Nnakasa bi da bi, sun bayyana a cikin bayanin da suka bayar cewa suna ci gaba da zama sahihan mambobin gudanarwa na APC, bayan an zabe su bisa ka’ida a lokacin taron jam’iyya na 2022. Sun bayyana cewa dakatarwar an yi ta ne saboda siyasa kuma tana da alaka da biyayyarsu ga jigon APC, Dakta Sani Abdullahi Shinkafi wanda ake cewa yana da matsala a dangantakarsa da wasu mutane masu rinjaye a cikin reshen jam’iyyar na jihar saboda tsayuwarsa kan ka’idojin dimokuradiyya wajen bin tsarin doka da sauran su. Mambobin suna neman sanarwa cewa “duk wani yunkuri na dakatarwa, korewa, tsoratarwa, cin zarafi ko kawar da membobinsu (Shinkafi, Ibrahim da Kurya) daga APC ta hannun wadanda ake kara (APC, Maikatako da Shinkafi) ko wani mutum kuma da ake kiransa da wani suna, ya saba wa doka, saba ka’ida, karya dokoki da kuma yin karfa-karfa.” Sai dai kuma kotu ba ta saka ranar fara sauraron wannan shari’a ba.

LABARAI MASU NASABA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

December 19, 2025
‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

December 19, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Tambarin Dimokuradiyya

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

November 28, 2025
Next Post
Binciken CGTN: Ya Kamata A Dauki Matakai Don Kula Da Yanayin Duniya

Binciken CGTN: Ya Kamata A Dauki Matakai Don Kula Da Yanayin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.