• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa

byKhalid Idris Doya
1 year ago
Auduga

Gwamnatin Jihar Gombe, na shirin farfado da Masana’antun Auduga ta hanyar rugumar shirin gwamnatin tarayya na farfado da noman auduga, don bunkasa tattalin arzikin al’ummar jihar.

Gwamnan Jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya ne ya bayyana hakan, yayin da yake gana wa da tawagar ‘Kamfanin Arise Integrated Industrial Platform’ karkashin jagorancin Babban Mataimakin Shugaban Kamfanin Jacky Ribiere, a fadar gwamnatin jihar ta Gombe.

  • Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli
  • Hajj 2024: NAHCON Ta Bukaci ‘Yan Jarida Su Yi Riko Da Gaskiya

Yahaya, wanda ya yi tsokaci a kan kokarin gwamnatin tarayya na sake farfado da noman auduga da masakun tufafi a Nijeriya, ya ba da tabbacin bayar da gagarumin goyon baya, domin saukaka farfado da noman na auduga a fadin jihar ta Gombe tare da yaba wa da kuma jaddada hangen nesan Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu a kan hakan.

Ya kara da cewa, kasancewar Gombe jiha ce mai samar da auduga da wasu takwarorinta na Arewa kamar Katsina, Kaduna, da kuma Zamfara, akwai fatan sake farfado da noman auduga tare da sarrafa Irinta kamar yadda shirin farfado da noman audugan na gwamnatin ya kuduri aniyar yi.

Gwamna Inuwa, ya sake jaddada muhimmancin hada hannu da masu ruwa da tsaki; wadanda suka hada da Kungiyar Manoman Auduga ta Kasa (NACOTAN), don samar da cikakken tsarin farfado da noma da kuma sarrafa audugar.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Haka zalika, ya bayyana damammakin da ake da su na damawa da manoma a Karamar Hukumar Balanga da wasu sauran Kananan Hukumomin Kudancin Jihar, wadanda suke da matukar muhimmanci wajen noman wannan auduga a jihar.

“Sake farfado da sana’ar noman auduga, zai magance rashin aikin yi a tsakanin matasan Nijeriya tare da farfado da tattalin arzikin wannan kasa,” in ji Gwamnan. Sannan, ya bayyana Jihar Gombe a matsayin daya daga cikin jihohin da ake noman audugar, ya kuma yi alkawarin ci gaba da ba da kwarin guiwa ga noman na auduga, domin samun riba mai yawan gaske.

Bugu da kari, ya kuma shaida wa bakin nasa cewa, ganin yadda aka kafa sansanin masana’antu na Muhammadu Buhari, mai fadin hekta 1,000 a kusa da tashar wutar lantarki ta Dadinkowa; mai karfin megawat 40 da kamfanonin gurzan auduga da ake da su a Jihar Gombe, hakan zai tallafa wajen sake farfado da bangaren noman na auduga.

Har ila yau, taron ya samu halartar Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, da Kwamishinan Ciniki, Masana’antu da Yawon Bude Ido, Nasiru Mohammed Aliyu da kuma takwaransa na Ma’aikatar Noma da Kiwo, Dakta Barnabas Malle; kamar yadda Ismaila Uba Misilli, Babban Daraktan Yada Labarun Gwamnan Jihar na Gombe ya nakalto.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?

Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?

LABARAI MASU NASABA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version