• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Gombe, na shirin farfado da Masana’antun Auduga ta hanyar rugumar shirin gwamnatin tarayya na farfado da noman auduga, don bunkasa tattalin arzikin al’ummar jihar.

Gwamnan Jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya ne ya bayyana hakan, yayin da yake gana wa da tawagar ‘Kamfanin Arise Integrated Industrial Platform’ karkashin jagorancin Babban Mataimakin Shugaban Kamfanin Jacky Ribiere, a fadar gwamnatin jihar ta Gombe.

  • Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli
  • Hajj 2024: NAHCON Ta Bukaci ‘Yan Jarida Su Yi Riko Da Gaskiya

Yahaya, wanda ya yi tsokaci a kan kokarin gwamnatin tarayya na sake farfado da noman auduga da masakun tufafi a Nijeriya, ya ba da tabbacin bayar da gagarumin goyon baya, domin saukaka farfado da noman na auduga a fadin jihar ta Gombe tare da yaba wa da kuma jaddada hangen nesan Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu a kan hakan.

Ya kara da cewa, kasancewar Gombe jiha ce mai samar da auduga da wasu takwarorinta na Arewa kamar Katsina, Kaduna, da kuma Zamfara, akwai fatan sake farfado da noman auduga tare da sarrafa Irinta kamar yadda shirin farfado da noman audugan na gwamnatin ya kuduri aniyar yi.

Gwamna Inuwa, ya sake jaddada muhimmancin hada hannu da masu ruwa da tsaki; wadanda suka hada da Kungiyar Manoman Auduga ta Kasa (NACOTAN), don samar da cikakken tsarin farfado da noma da kuma sarrafa audugar.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

Haka zalika, ya bayyana damammakin da ake da su na damawa da manoma a Karamar Hukumar Balanga da wasu sauran Kananan Hukumomin Kudancin Jihar, wadanda suke da matukar muhimmanci wajen noman wannan auduga a jihar.

“Sake farfado da sana’ar noman auduga, zai magance rashin aikin yi a tsakanin matasan Nijeriya tare da farfado da tattalin arzikin wannan kasa,” in ji Gwamnan. Sannan, ya bayyana Jihar Gombe a matsayin daya daga cikin jihohin da ake noman audugar, ya kuma yi alkawarin ci gaba da ba da kwarin guiwa ga noman na auduga, domin samun riba mai yawan gaske.

Bugu da kari, ya kuma shaida wa bakin nasa cewa, ganin yadda aka kafa sansanin masana’antu na Muhammadu Buhari, mai fadin hekta 1,000 a kusa da tashar wutar lantarki ta Dadinkowa; mai karfin megawat 40 da kamfanonin gurzan auduga da ake da su a Jihar Gombe, hakan zai tallafa wajen sake farfado da bangaren noman na auduga.

Har ila yau, taron ya samu halartar Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, da Kwamishinan Ciniki, Masana’antu da Yawon Bude Ido, Nasiru Mohammed Aliyu da kuma takwaransa na Ma’aikatar Noma da Kiwo, Dakta Barnabas Malle; kamar yadda Ismaila Uba Misilli, Babban Daraktan Yada Labarun Gwamnan Jihar na Gombe ya nakalto.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GombeNoman Auduga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karancin Abinci Na Kara Ta’azzara A Nijeriya

Next Post

Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?

Related

Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

7 days ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

7 days ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

3 weeks ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?

Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.