ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kananan Yara Fiye Da Miliyan 5 Sun Mutu A 2021- Majalisar Dinkin Duniya

by Sadiq
3 years ago
Yara

Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya, ya bayyana yadda kanana yara akalla miliyan biyar ’yan shekara biyar zuwa kasa suka rasa rayukansu cikin shekarar 2021, kari kan matasa ‘yan shekaru biyar zuwa 24 su kimanin miliyan daya da dubu dari da suka mutu duk dai a shekarar.

Gamayyar kungiyoyin Majalisar Dinkin Duniya da ke tattara alkaluman mace-macen yara UNIGME cikin mabanbantan rahoton da suka fitar cikin makon nan, sun bayyana cewa yaro guda na mutuwa a duk dakika hudu da digo hudu wanda ke nuna asarar asarar yara fiye da miliyan biyar cikin shekarar 2021 duk da cewa shekarar ta kasance mafi karancin asarar rayukan jarirai da aka gani tun bayan shekarar 2000.

  • Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma’aikata A Kaduna
  • Tawagar Manyan Malaman Addinin Musulunci Ta Ziyarci Urumqi Na Xinjiang

A cewar gamayyar rahoton a tsakanin lokacin da yaran fiye da miliyan biyar da kuma matasa miliyan daya da dubu dari daya suka mutu cikin shekarar ta 2021 an kuma haifi jarirai akalla miliyan daya da dubu dari tara kuma galibinsu sun samu kulawar da ta basu damar tsallake yawaitar mace-macen sabbin haihuwar da ake samu.

ADVERTISEMENT

Kungiyoyin sun bayyana cewa matakan da gwamnatoci suka dauka na bunkasa bangarorin lafiya kama daga sashen haihuwa da kuma kula da sabbin haihuwar baya ga yaran da suka fara tasawa ya taimaka matuka wajen rasa asarar rayukan matasa daga haihuwa zuwa shekaru 24 a duniya.

Daraktan tattara bayanai na UNICEF, Vidhya Ganesh ta bayyana cewa, wajibi ne gwamnatoci su zage damtse wajen bunkasa bangarorin lafiya don dakile rasa rayukan babu gaira babu dalili musamman ga yara sabbin haihuwa zuwa shekaru biyar.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

A cewar Vidhya Ganesh, mace-macen kananan yara ya ragu da akalla kashi 50 karon farko cikin wannan karni inda mace-macen matasa ya ragu da kashi 36 yayin da mace-macen sabbin haihuwa shi kuma ya ragu da kashi 35.

Sai dai Dakta Anshu Banerjee daraktan sashen kula da mace-macen sabbin haihuwa da matasa na WHO, ya bayyana cewa duk da wannan kankanuwar nasarar, wajibi ne gwamnatoci su mike tsaye wajen bunkasa bangarorin lafiya daidai lokacin da alkaluma ke nuna yiwuwar rasa rayukan kananan yara da matasa miliyan 56 nan da sekarar 2030 kari kan sabbin haihuwa miliyan 16 da za su iya mutuwa kafin wannan lokaci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN
Manyan Labarai

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Next Post
Mun Biya Biliyan 173.2 Kudin Daidaita Farashin Man Fetur Cikin Shekara 4 – Gwamnati

Mun Biya Biliyan 173.2 Kudin Daidaita Farashin Man Fetur Cikin Shekara 4 - Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.