• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kananan Yara Fiye Da Miliyan 5 Sun Mutu A 2021- Majalisar Dinkin Duniya

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kananan Yara Fiye Da Miliyan 5 Sun Mutu A 2021- Majalisar Dinkin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya, ya bayyana yadda kanana yara akalla miliyan biyar ’yan shekara biyar zuwa kasa suka rasa rayukansu cikin shekarar 2021, kari kan matasa ‘yan shekaru biyar zuwa 24 su kimanin miliyan daya da dubu dari da suka mutu duk dai a shekarar.

Gamayyar kungiyoyin Majalisar Dinkin Duniya da ke tattara alkaluman mace-macen yara UNIGME cikin mabanbantan rahoton da suka fitar cikin makon nan, sun bayyana cewa yaro guda na mutuwa a duk dakika hudu da digo hudu wanda ke nuna asarar asarar yara fiye da miliyan biyar cikin shekarar 2021 duk da cewa shekarar ta kasance mafi karancin asarar rayukan jarirai da aka gani tun bayan shekarar 2000.

  • Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma’aikata A Kaduna
  • Tawagar Manyan Malaman Addinin Musulunci Ta Ziyarci Urumqi Na Xinjiang

A cewar gamayyar rahoton a tsakanin lokacin da yaran fiye da miliyan biyar da kuma matasa miliyan daya da dubu dari daya suka mutu cikin shekarar ta 2021 an kuma haifi jarirai akalla miliyan daya da dubu dari tara kuma galibinsu sun samu kulawar da ta basu damar tsallake yawaitar mace-macen sabbin haihuwar da ake samu.

Kungiyoyin sun bayyana cewa matakan da gwamnatoci suka dauka na bunkasa bangarorin lafiya kama daga sashen haihuwa da kuma kula da sabbin haihuwar baya ga yaran da suka fara tasawa ya taimaka matuka wajen rasa asarar rayukan matasa daga haihuwa zuwa shekaru 24 a duniya.

Daraktan tattara bayanai na UNICEF, Vidhya Ganesh ta bayyana cewa, wajibi ne gwamnatoci su zage damtse wajen bunkasa bangarorin lafiya don dakile rasa rayukan babu gaira babu dalili musamman ga yara sabbin haihuwa zuwa shekaru biyar.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

A cewar Vidhya Ganesh, mace-macen kananan yara ya ragu da akalla kashi 50 karon farko cikin wannan karni inda mace-macen matasa ya ragu da kashi 36 yayin da mace-macen sabbin haihuwa shi kuma ya ragu da kashi 35.

Sai dai Dakta Anshu Banerjee daraktan sashen kula da mace-macen sabbin haihuwa da matasa na WHO, ya bayyana cewa duk da wannan kankanuwar nasarar, wajibi ne gwamnatoci su mike tsaye wajen bunkasa bangarorin lafiya daidai lokacin da alkaluma ke nuna yiwuwar rasa rayukan kananan yara da matasa miliyan 56 nan da sekarar 2030 kari kan sabbin haihuwa miliyan 16 da za su iya mutuwa kafin wannan lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JariraiMajalisar Dinkin DuniyaRahotoYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma’aikata A Kaduna

Next Post

Mun Biya Biliyan 173.2 Kudin Daidaita Farashin Man Fetur Cikin Shekara 4 – Gwamnati

Related

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

2 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

3 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

5 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

19 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

22 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

1 day ago
Next Post
Mun Biya Biliyan 173.2 Kudin Daidaita Farashin Man Fetur Cikin Shekara 4 – Gwamnati

Mun Biya Biliyan 173.2 Kudin Daidaita Farashin Man Fetur Cikin Shekara 4 - Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.