• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kananan Yara Fiye Da Miliyan 5 Sun Mutu A 2021- Majalisar Dinkin Duniya

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kananan Yara Fiye Da Miliyan 5 Sun Mutu A 2021- Majalisar Dinkin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya, ya bayyana yadda kanana yara akalla miliyan biyar ’yan shekara biyar zuwa kasa suka rasa rayukansu cikin shekarar 2021, kari kan matasa ‘yan shekaru biyar zuwa 24 su kimanin miliyan daya da dubu dari da suka mutu duk dai a shekarar.

Gamayyar kungiyoyin Majalisar Dinkin Duniya da ke tattara alkaluman mace-macen yara UNIGME cikin mabanbantan rahoton da suka fitar cikin makon nan, sun bayyana cewa yaro guda na mutuwa a duk dakika hudu da digo hudu wanda ke nuna asarar asarar yara fiye da miliyan biyar cikin shekarar 2021 duk da cewa shekarar ta kasance mafi karancin asarar rayukan jarirai da aka gani tun bayan shekarar 2000.

  • Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma’aikata A Kaduna
  • Tawagar Manyan Malaman Addinin Musulunci Ta Ziyarci Urumqi Na Xinjiang

A cewar gamayyar rahoton a tsakanin lokacin da yaran fiye da miliyan biyar da kuma matasa miliyan daya da dubu dari daya suka mutu cikin shekarar ta 2021 an kuma haifi jarirai akalla miliyan daya da dubu dari tara kuma galibinsu sun samu kulawar da ta basu damar tsallake yawaitar mace-macen sabbin haihuwar da ake samu.

Kungiyoyin sun bayyana cewa matakan da gwamnatoci suka dauka na bunkasa bangarorin lafiya kama daga sashen haihuwa da kuma kula da sabbin haihuwar baya ga yaran da suka fara tasawa ya taimaka matuka wajen rasa asarar rayukan matasa daga haihuwa zuwa shekaru 24 a duniya.

Daraktan tattara bayanai na UNICEF, Vidhya Ganesh ta bayyana cewa, wajibi ne gwamnatoci su zage damtse wajen bunkasa bangarorin lafiya don dakile rasa rayukan babu gaira babu dalili musamman ga yara sabbin haihuwa zuwa shekaru biyar.

Labarai Masu Nasaba

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

A cewar Vidhya Ganesh, mace-macen kananan yara ya ragu da akalla kashi 50 karon farko cikin wannan karni inda mace-macen matasa ya ragu da kashi 36 yayin da mace-macen sabbin haihuwa shi kuma ya ragu da kashi 35.

Sai dai Dakta Anshu Banerjee daraktan sashen kula da mace-macen sabbin haihuwa da matasa na WHO, ya bayyana cewa duk da wannan kankanuwar nasarar, wajibi ne gwamnatoci su mike tsaye wajen bunkasa bangarorin lafiya daidai lokacin da alkaluma ke nuna yiwuwar rasa rayukan kananan yara da matasa miliyan 56 nan da sekarar 2030 kari kan sabbin haihuwa miliyan 16 da za su iya mutuwa kafin wannan lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JariraiMajalisar Dinkin DuniyaRahotoYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma’aikata A Kaduna

Next Post

Mun Biya Biliyan 173.2 Kudin Daidaita Farashin Man Fetur Cikin Shekara 4 – Gwamnati

Related

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

17 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

2 days ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

2 days ago
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

2 days ago
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
Manyan Labarai

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

2 days ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

2 days ago
Next Post
Mun Biya Biliyan 173.2 Kudin Daidaita Farashin Man Fetur Cikin Shekara 4 – Gwamnati

Mun Biya Biliyan 173.2 Kudin Daidaita Farashin Man Fetur Cikin Shekara 4 - Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.