ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kananan Yara Fiye Da Miliyan 5 Sun Mutu A 2021- Majalisar Dinkin Duniya

by Sadiq
4 years ago
Yara

Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya, ya bayyana yadda kanana yara akalla miliyan biyar ’yan shekara biyar zuwa kasa suka rasa rayukansu cikin shekarar 2021, kari kan matasa ‘yan shekaru biyar zuwa 24 su kimanin miliyan daya da dubu dari da suka mutu duk dai a shekarar.

Gamayyar kungiyoyin Majalisar Dinkin Duniya da ke tattara alkaluman mace-macen yara UNIGME cikin mabanbantan rahoton da suka fitar cikin makon nan, sun bayyana cewa yaro guda na mutuwa a duk dakika hudu da digo hudu wanda ke nuna asarar asarar yara fiye da miliyan biyar cikin shekarar 2021 duk da cewa shekarar ta kasance mafi karancin asarar rayukan jarirai da aka gani tun bayan shekarar 2000.

  • Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma’aikata A Kaduna
  • Tawagar Manyan Malaman Addinin Musulunci Ta Ziyarci Urumqi Na Xinjiang

A cewar gamayyar rahoton a tsakanin lokacin da yaran fiye da miliyan biyar da kuma matasa miliyan daya da dubu dari daya suka mutu cikin shekarar ta 2021 an kuma haifi jarirai akalla miliyan daya da dubu dari tara kuma galibinsu sun samu kulawar da ta basu damar tsallake yawaitar mace-macen sabbin haihuwar da ake samu.

ADVERTISEMENT

Kungiyoyin sun bayyana cewa matakan da gwamnatoci suka dauka na bunkasa bangarorin lafiya kama daga sashen haihuwa da kuma kula da sabbin haihuwar baya ga yaran da suka fara tasawa ya taimaka matuka wajen rasa asarar rayukan matasa daga haihuwa zuwa shekaru 24 a duniya.

Daraktan tattara bayanai na UNICEF, Vidhya Ganesh ta bayyana cewa, wajibi ne gwamnatoci su zage damtse wajen bunkasa bangarorin lafiya don dakile rasa rayukan babu gaira babu dalili musamman ga yara sabbin haihuwa zuwa shekaru biyar.

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

A cewar Vidhya Ganesh, mace-macen kananan yara ya ragu da akalla kashi 50 karon farko cikin wannan karni inda mace-macen matasa ya ragu da kashi 36 yayin da mace-macen sabbin haihuwa shi kuma ya ragu da kashi 35.

Sai dai Dakta Anshu Banerjee daraktan sashen kula da mace-macen sabbin haihuwa da matasa na WHO, ya bayyana cewa duk da wannan kankanuwar nasarar, wajibi ne gwamnatoci su mike tsaye wajen bunkasa bangarorin lafiya daidai lokacin da alkaluma ke nuna yiwuwar rasa rayukan kananan yara da matasa miliyan 56 nan da sekarar 2030 kari kan sabbin haihuwa miliyan 16 da za su iya mutuwa kafin wannan lokaci.

MASU ALAKA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Next Post
Mun Biya Biliyan 173.2 Kudin Daidaita Farashin Man Fetur Cikin Shekara 4 – Gwamnati

Mun Biya Biliyan 173.2 Kudin Daidaita Farashin Man Fetur Cikin Shekara 4 - Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.