• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kayan Makulashen Hausawa Na Zamani

by Bilkisu Tijjani
3 years ago
in Rahotonni
0
Kayan Makulashen Hausawa Na Zamani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai rukuni na abincin Hausawa wadanda su Hausawan ne suke yi ba tare da sun gani daga wata al’umma ba, sai dai kawai don ci gaban zamani ne ya haifar da samuwarsu.

Idan aka kula za a gani wasu daga cikin kayayyakin hadin su ba na gargajiya ba ne na zamani ne, amma za mu fahinci sun yi amfani da basirarsu ta zamani ne suka kirkiro su, kamar yadda aka samu na garajiya. Ga dai kamar haka;

  • Alkawurana Ga ‘Yan Nijeriya Kan Tsaro, Zaman Kashe Wando Da Tattalin Arziki — Kwankwaso
  • Hadari Gabas… Tsugune Ba Ta Kare Ba A  Jam’iyyar PDP

Hallaka Kobo,

Kayan hadinsa: Sukari, Gyada. Ga kuma yadda ake hadawa:

A samu tukunya a dora a wuta, sai a zuba sukari a yi ta juyawa har sai sukarin ya narke sai a debo gyada dai-dai misali a zuba a yi ta juyawa har sai ya hade jikinsa. Sannan a samo tire a shafa masa man gyada. Bayan haka, sai a juye sukarin, idan ya dan sha iska sai a sa wuka a yayyanka yadda ake so, in an yi haka an kammala yin Hallaka Kwabo.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Hanjin Ligidi

Kayan hadinsa: Sukari, Tsamiya, ga kuma yadda ake hadawa:

A mataki na farko sai a samu jarida ko wata takarda mai girma a yayyanka a nade kamar yadda kaho yake, wato kasan ya yi tsini sama kuma ya bude, a sa kasa a roba ko wani abu mai fadi da zai dauki kasar a soka jaridar da aka nade din a cikin kasar. Sannan sai a jika tsamiya a ajiye a gefe, a samu tukunya a zuba sukarin a ciki a dora a kan wuta a yi ta juyawa har sai sukarin ya narke sai a dauko ruwan tsamiyar da aka jika a zuba a kai, za a ga ya taso sai a yi ta juyawa har sai ya hadu, sai a rika diba ana zubawa cikin jaridar da aka nada daidai gwargwado ana kuma saka masa tsinke a cikin kowanne.

Alewar Madara

Kayan hadi: Madarar gari, Sukari, da Filebo. Ga kuma yadda ake hadawa:

A mataki na farko sai a dora ruwa dan daidai a wuta sai a zuba sukari ya tafasa har sai ruwan ya yi kauri, sai a zuba filebo kadan a kawo madara ana zubawa ana tukawa kamar yadda ake tuka tuwo har sai ya yi tauri dai-dai misali, kar ya yi ruwa, sai a nemi tire a shafa man gyada sai a zuba dafaffen sukarin a kai a yanka daidai yadda ake so.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HausawaKayan MakulasheZamani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanyoyin Amfani Da Kayan Kwalliya Na ‘Corset’

Next Post

Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida

Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.