• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kayan Makulashen Hausawa Na Zamani

by Bilkisu Tijjani
3 years ago
in Rahotonni
0
Kayan Makulashen Hausawa Na Zamani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai rukuni na abincin Hausawa wadanda su Hausawan ne suke yi ba tare da sun gani daga wata al’umma ba, sai dai kawai don ci gaban zamani ne ya haifar da samuwarsu.

Idan aka kula za a gani wasu daga cikin kayayyakin hadin su ba na gargajiya ba ne na zamani ne, amma za mu fahinci sun yi amfani da basirarsu ta zamani ne suka kirkiro su, kamar yadda aka samu na garajiya. Ga dai kamar haka;

  • Alkawurana Ga ‘Yan Nijeriya Kan Tsaro, Zaman Kashe Wando Da Tattalin Arziki — Kwankwaso
  • Hadari Gabas… Tsugune Ba Ta Kare Ba A  Jam’iyyar PDP

Hallaka Kobo,

Kayan hadinsa: Sukari, Gyada. Ga kuma yadda ake hadawa:

A samu tukunya a dora a wuta, sai a zuba sukari a yi ta juyawa har sai sukarin ya narke sai a debo gyada dai-dai misali a zuba a yi ta juyawa har sai ya hade jikinsa. Sannan a samo tire a shafa masa man gyada. Bayan haka, sai a juye sukarin, idan ya dan sha iska sai a sa wuka a yayyanka yadda ake so, in an yi haka an kammala yin Hallaka Kwabo.

Labarai Masu Nasaba

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

Hanjin Ligidi

Kayan hadinsa: Sukari, Tsamiya, ga kuma yadda ake hadawa:

A mataki na farko sai a samu jarida ko wata takarda mai girma a yayyanka a nade kamar yadda kaho yake, wato kasan ya yi tsini sama kuma ya bude, a sa kasa a roba ko wani abu mai fadi da zai dauki kasar a soka jaridar da aka nade din a cikin kasar. Sannan sai a jika tsamiya a ajiye a gefe, a samu tukunya a zuba sukarin a ciki a dora a kan wuta a yi ta juyawa har sai sukarin ya narke sai a dauko ruwan tsamiyar da aka jika a zuba a kai, za a ga ya taso sai a yi ta juyawa har sai ya hadu, sai a rika diba ana zubawa cikin jaridar da aka nada daidai gwargwado ana kuma saka masa tsinke a cikin kowanne.

Alewar Madara

Kayan hadi: Madarar gari, Sukari, da Filebo. Ga kuma yadda ake hadawa:

A mataki na farko sai a dora ruwa dan daidai a wuta sai a zuba sukari ya tafasa har sai ruwan ya yi kauri, sai a zuba filebo kadan a kawo madara ana zubawa ana tukawa kamar yadda ake tuka tuwo har sai ya yi tauri dai-dai misali, kar ya yi ruwa, sai a nemi tire a shafa man gyada sai a zuba dafaffen sukarin a kai a yanka daidai yadda ake so.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HausawaKayan MakulasheZamani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanyoyin Amfani Da Kayan Kwalliya Na ‘Corset’

Next Post

Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida

Related

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

2 months ago
Next Post
Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida

Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida

LABARAI MASU NASABA

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.