ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noman Auduga Na Ci Gaba Da Fuskantar Matsaloli – Cewar Masana

by Abubakar Abba
4 years ago
Auduga

Noman auduga a kasar nan, musamman a Arewacin Nijeriya na da cikakken tarihi, a yankin idan yik la’akari da irin gudunmawar da fannin ya samar wajen bunkasa tattalin arzikin a yankin tun kafin Nijeriya ta samu ‘yancin kanta daga gun turawan mulkin mallaka. 

Har ila yau, tarihi ya nuna cewa, noman na Audugar a kasar nan, bayan samun ‘yancin kan Na kasar, fannin ya taimaka matuka wajen habaka tattalin arzikin kasar baki daya. 

  • Da Dumi-Dumi: Sarauniyar Ingila, Elizabeth Ta Rasu
  • Da Dumi-dumi: Shugaban Kwamitin Amintattu Na PDP Yayi Murabus

Sai dai, wani abin takaici shine, wasu masana a noman na Audugar a kasar nan, sun daidaitu a kan cewa, har yanzu da akwai alamun da ke nuna cewa, fannin na noman audugar a kasar nan, na fuskantar wasu manyan kalubalen da ke ci gaba da janyo wa fannin koma baya. 

ADVERTISEMENT

A bisa hasashen da masanan suka yi, har yanzu ba a samu canjin da zai sa kasar nan ta shiga cikin sahun kasashen duniya da suka yi fice a harkar noman Auduga ba, musamman idan aka yi dubi da yadda samar da ingantaccen Irin noman Audugar a kasar ya janyo fannin a ‘yan shekarun baya, ke fuskantar barazana. 

A cewar masanan, wannan halin ya sa ana barin Audugar da aka noma a kasar aka kuma kai ketare don sayar wa, ba ta cika samun karbuwar da ake bukata ba a kasuwar ta duniya. 

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Sai dai, idan aka yi la’akari da yadda wasu cibiyiyin da ke gudanar da bincike a bangaren samar da ingantaccen irin noman na Audugar a kasar nan suka yunkuro, za a iya cewa, a yanzu Nijeriya ta dora dambar bunkasa nomanta, musamman domin ta samu karbuwa a kasuwar ta duniya. 

Masanan sun sanar da cewa, a shekarun baya ana tantance ingantacciyar audugar wanda hakan ya taimaka wa, fannin Da kima manoman na audugar a kasar nan, musamman domin ta yi Daraja a kasuwar duniya Sai dai, masanan sun bayyana cewa, a bisa yunkurin da cibiyoyin gudanar da da bincike suka yi don tantance ingantaccen Irin na Audugar a kasar nan, zai taimaka wajen kara farfado da nomanta a kasar, inda hakan zai taimaka don Audugar da ake noma wa a kara ta yi Kunnen Doki da sauran wacce sauran kasashen duniya ke kai wa kasuwar ta duniya domin sayarwa. 

A cewar su, akwai kuma bukatar gwamnatin tarayya ta zuba kudade masu yawa domin cibiyoyin su kara zage wajen gudanar da bincike don a samar da ingantaccen Irin na Audugar a kasar nan. 

Misali, don a tabbatar da an samar da ingantaccen irin na audugar, a kwanan baya ne Cibiyar Binciken Aikin Gona ta Jami’ar Ahmadu Bello, ta kuduri aniyar samar da ingantaccen Irin na Audugar wanda kuma cibiyar ta ce, hakan zai taimaka matuka wajen kara farfado da nomanta a kasar nan. 

Cibiyar za ta yi nazarin ingancin irin da noman da kasuwancinta da matsaloli da Masanan sun yi nuni da cewa, rashin samar da ingantaccen tsari a fannin na noman audugar a kasar nan, na daya daga cikin matsalolin da fannin a kasar nan ke fuskanta.

Auduga
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Ko Talakawa Na Amfana Da Yawaitar Sauya Shekar ’Yan Siyasa?

Ko Talakawa Na Amfana Da Yawaitar Sauya Shekar ’Yan Siyasa?

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.