• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kudirin Wa’adin Shekaru 6 Ga Shugaban Kasa Ya Tsallake Karatu Na Farko

bySulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
majalisar kasa

Majalisar wakilai ta yi karatu na farko a kan kudirin dokar da ta gabatar na gyaran kundin tsarin mulkin kasar na shekarar 1999, domin gabatar da wa’adin mulki daya na shekara 6 ga shugaban kasa da gwamnonin jihohi da shugabannin kananan hukumomi.

 

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Ideato ta arewa /Ideato ta Kudu a Jihar Imo, tare da wasu ‘yan majalisa 50 ne suka gabatar da kudirin da na nufin rage kudaden da ake kashewa kan zabe ta hanyar rage wa’adin wadannan ofisoshi.

  • Tsaro: Gwamnatin Tinubu Ta Kashe Naira Tiriliyan 3.2 A Shekara Daya
  • Martani: Ba Hannu Na A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa – Hon Boza

Sauye-sauyen na da niyya shafar sashe na 7, 135, 137, 180, da 182 (1) na kundin tsarin mulki na 1999.

 

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Sashi na biyu na kudirin ya nemi a gyara sashe na 7 na dokar ta hanyar shigar da wani sabon sashe na 5 bayan karamin sashe na 4, wanda sashe na 5 ke cewa, “Duk wani mai rike da mukamin shugaban karamar hukuma zai bar ofishinsa a lokacin da wa’adinsa ya kare na shekaru 6 daga ranar da aka zabe shi.”

 

Sashe na 3 na kudirin yana neman a gyara sashe na 135 (2), (2A) da (3) na kundin tsarin mulki domin maye gurbin kalmar “hudu” zuwa “shida”.

 

Dangane da tanadin karamin sashe (1) na wannan kudirin, shugaban kasa zai bar ofishinsa a karshen wa’adin zangon shekaru shida (6) lokacin da aka zabe shi. Idan kuma aka zabe mutum a matsayin shugaban kasa har aka rantsar da shi a karkashin wannan tsarin, to za a kara gudanar da zabe, sannan za a yi la’akari da lokacin da aka fara rantsar da na farko ne.

 

Haka kuma kudirin ya bayyana cewa idan ana fama da yaki a Nijeriya, shugaban kasa yi la’akari da haka ya ki gudanar da zabe, amma majalisa na iya kari sama da shekara 6 lokaci bayan lokaci bisa karamin sashi na 2, sai dai karin ba zai wuce wata shida ba a ko wani lokaci.

 

Sashe na 4 na dudirin yana neman gyara sashe na 137 na kundin tsarin Nijeriya ta hanyar share sakin layi (b) da sake lambobi.
Sashe na 5 na kudirin da aka gabatar na neman gyara sashe na 180 na tsarin mulki ta hanyar goge wasu kananan sashe na 2 da na 3 tare da maye gurbinsu da sabon sashe na 2 da 3.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Sin Ta Kira Taron Binciken Manufofin Gaggauta Aikin Raya Yankin Yammacin Kasar

Sin Ta Kira Taron Binciken Manufofin Gaggauta Aikin Raya Yankin Yammacin Kasar

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version