• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kudirin Wa’adin Shekaru 6 Ga Shugaban Kasa Ya Tsallake Karatu Na Farko

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar wakilai ta yi karatu na farko a kan kudirin dokar da ta gabatar na gyaran kundin tsarin mulkin kasar na shekarar 1999, domin gabatar da wa’adin mulki daya na shekara 6 ga shugaban kasa da gwamnonin jihohi da shugabannin kananan hukumomi.

 

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Ideato ta arewa /Ideato ta Kudu a Jihar Imo, tare da wasu ‘yan majalisa 50 ne suka gabatar da kudirin da na nufin rage kudaden da ake kashewa kan zabe ta hanyar rage wa’adin wadannan ofisoshi.

  • Tsaro: Gwamnatin Tinubu Ta Kashe Naira Tiriliyan 3.2 A Shekara Daya
  • Martani: Ba Hannu Na A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa – Hon Boza

Sauye-sauyen na da niyya shafar sashe na 7, 135, 137, 180, da 182 (1) na kundin tsarin mulki na 1999.

 

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Sashi na biyu na kudirin ya nemi a gyara sashe na 7 na dokar ta hanyar shigar da wani sabon sashe na 5 bayan karamin sashe na 4, wanda sashe na 5 ke cewa, “Duk wani mai rike da mukamin shugaban karamar hukuma zai bar ofishinsa a lokacin da wa’adinsa ya kare na shekaru 6 daga ranar da aka zabe shi.”

 

Sashe na 3 na kudirin yana neman a gyara sashe na 135 (2), (2A) da (3) na kundin tsarin mulki domin maye gurbin kalmar “hudu” zuwa “shida”.

 

Dangane da tanadin karamin sashe (1) na wannan kudirin, shugaban kasa zai bar ofishinsa a karshen wa’adin zangon shekaru shida (6) lokacin da aka zabe shi. Idan kuma aka zabe mutum a matsayin shugaban kasa har aka rantsar da shi a karkashin wannan tsarin, to za a kara gudanar da zabe, sannan za a yi la’akari da lokacin da aka fara rantsar da na farko ne.

 

Haka kuma kudirin ya bayyana cewa idan ana fama da yaki a Nijeriya, shugaban kasa yi la’akari da haka ya ki gudanar da zabe, amma majalisa na iya kari sama da shekara 6 lokaci bayan lokaci bisa karamin sashi na 2, sai dai karin ba zai wuce wata shida ba a ko wani lokaci.

 

Sashe na 4 na dudirin yana neman gyara sashe na 137 na kundin tsarin Nijeriya ta hanyar share sakin layi (b) da sake lambobi.
Sashe na 5 na kudirin da aka gabatar na neman gyara sashe na 180 na tsarin mulki ta hanyar goge wasu kananan sashe na 2 da na 3 tare da maye gurbinsu da sabon sashe na 2 da 3.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Sadarwa

Next Post

Sin Ta Kira Taron Binciken Manufofin Gaggauta Aikin Raya Yankin Yammacin Kasar

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Shugaban kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Sin Ta Kira Taron Binciken Manufofin Gaggauta Aikin Raya Yankin Yammacin Kasar

Sin Ta Kira Taron Binciken Manufofin Gaggauta Aikin Raya Yankin Yammacin Kasar

LABARAI MASU NASABA

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.