• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP Ta Cika Shekara Daya Da Fara Gabatar Da Shirye-shiryen PODCAST

by Bello Hamza
3 years ago
LEADERSHIP

A ranar Laraba 22 ga watan Yuni 2022 Kamfanin LEADERSHIP ya cika shekara daya da fara gabatar da shirye-shirye ta hanyar manhajar PODCAST daga dakin watsa shiriye-shirye na zamani na LAST WORD a Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya.

Mahukuntan kamfanin LEADRSHIP sun yi alkawarin kara inganta ayyukan bangaren don jagorantar kafafen watsa labarai na kasar nan a fannin yada labarai ta hanyoyi na zamani, musamman ganin yadda al’umma ke kishi da fatan samun sahihan labarai.

  • Mun Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kai Hari A Cocin Katolika Dake Ondo – Amotekun

Da yake tsokaci a kan cikar sashin shekara daya da kafuwa, shugaban shashen yada labarai na Kamfanin LEADERSHIP, Mista Bayo Amodu, ya ce, “shirye-shiryenmu na Podcast sun samar da mahanga ta musamman a tsarin gabatar da shirye-shirye ta kafafen sadarwa na zamani tun da aka kafa ta, don haka muna yi wa masu bibiyarmu alkawarin inganta yadda ake gabatar da shirye-shirye don samar musu da hirye-shirye masu kayatarwa, ilimantarwa da fadakarwa a cikin shekaru masu zuwa.
“A ranar Laraba 22 ga watan Yuni 2022, aka fara gabatar da shirye-shirye daga dakin watsa shirye-shiryenmu na Podcast.

Dalilan fara shirin ta hanyar wannan tsari shi ne yadda muka lura da cewa, bangaren gabatar da shirye-shirye ta kafafen sadarwa na zamani babu kwararrun ‘yan jarida a ciki, galibin masu yi suna kiran kansu da sunaye iri iri, ba sa yin cikakken bincike wajen gabatar da labarunsu, ta haka kuma suke watsa labarai marasa inganci ga al’umma.

“Ina sane da wurare daban-daban da labarun kanzon kurege suka haifar da matsaloli ga al’ummar Nijeriya da dama. Amma mu a Kamfanin LEADERSHIP an san mu da samar da ingattun labarai, mun kuma dade a fagen harkar watsa labarai a kan haka muka shigo don cike gurbin da al’umma ke bukata a fagen watsa labarai ta kafafen sadarwa na zamani.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

“Mun yi gaggarumin kokari a cikin shekarar da ta wuce. Mun samar da tsari na musamman a bangaren aikin jarida ta kafafen sadarwa na zamani, yawan mutane da ke bibiyarmu da kuma sakonnin da muke samu a kullum shaida ne ga yada aka karbe mu, yana kuma nuna irin kokarinmu a wannan fagen.
“Mun samar da shirye-shirye da dama, muna ci gaba da inganta su tare da tsayuwa a kan bayar da sahihan labarai. Za mu nisanci dukkan nau’in labarun kazon kurege, za kuma mu tabbatar da kowa ya samu hakkin fadar albarkacin bakinsa a dukkan lokaci,” in ji shi.

Mista Amodu ya kuma bayana cewa, bayan shirye-shirye ta Podcast, Kamfanin LEADERSHIP Group Limited, na kuma jagorantar buga Jaridar LEADERSHIP Daily, LEADERSHIP Weekend, LEADERSHIP Sunday, LEADERSHIP Hausa da kuma National Economy.

Daga cikin manya manyan shirye shiryen da ake gabatarwa a dakin watsa shirye-shiryen na LAST WORD akwai shirin sashashin Hausa na LEADERSHIP mai lakabin ‘BARKA DA HANTSI NIJERIYA’ wanda ake gabatarwa da misalin karfe 9 na safe daga Litinin har zuwa Juma’a kai-tsaye ta kafofin Facebook a “Leadership Hausa”, YouTube a “Leadership Hausa”, sai kafar Twitter a “@Leadershiphausa”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

LABARAI MASU NASABA

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.