• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP Ta Cika Shekara Daya Da Fara Gabatar Da Shirye-shiryen PODCAST

by Bello Hamza
3 years ago
in Rahotonni
0
LEADERSHIP Ta Cika Shekara Daya Da Fara Gabatar Da Shirye-shiryen PODCAST
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Laraba 22 ga watan Yuni 2022 Kamfanin LEADERSHIP ya cika shekara daya da fara gabatar da shirye-shirye ta hanyar manhajar PODCAST daga dakin watsa shiriye-shirye na zamani na LAST WORD a Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya.

Mahukuntan kamfanin LEADRSHIP sun yi alkawarin kara inganta ayyukan bangaren don jagorantar kafafen watsa labarai na kasar nan a fannin yada labarai ta hanyoyi na zamani, musamman ganin yadda al’umma ke kishi da fatan samun sahihan labarai.

  • Mun Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kai Hari A Cocin Katolika Dake Ondo – Amotekun

Da yake tsokaci a kan cikar sashin shekara daya da kafuwa, shugaban shashen yada labarai na Kamfanin LEADERSHIP, Mista Bayo Amodu, ya ce, “shirye-shiryenmu na Podcast sun samar da mahanga ta musamman a tsarin gabatar da shirye-shirye ta kafafen sadarwa na zamani tun da aka kafa ta, don haka muna yi wa masu bibiyarmu alkawarin inganta yadda ake gabatar da shirye-shirye don samar musu da hirye-shirye masu kayatarwa, ilimantarwa da fadakarwa a cikin shekaru masu zuwa.
“A ranar Laraba 22 ga watan Yuni 2022, aka fara gabatar da shirye-shirye daga dakin watsa shirye-shiryenmu na Podcast.

Dalilan fara shirin ta hanyar wannan tsari shi ne yadda muka lura da cewa, bangaren gabatar da shirye-shirye ta kafafen sadarwa na zamani babu kwararrun ‘yan jarida a ciki, galibin masu yi suna kiran kansu da sunaye iri iri, ba sa yin cikakken bincike wajen gabatar da labarunsu, ta haka kuma suke watsa labarai marasa inganci ga al’umma.

“Ina sane da wurare daban-daban da labarun kanzon kurege suka haifar da matsaloli ga al’ummar Nijeriya da dama. Amma mu a Kamfanin LEADERSHIP an san mu da samar da ingattun labarai, mun kuma dade a fagen harkar watsa labarai a kan haka muka shigo don cike gurbin da al’umma ke bukata a fagen watsa labarai ta kafafen sadarwa na zamani.

Labarai Masu Nasaba

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

“Mun yi gaggarumin kokari a cikin shekarar da ta wuce. Mun samar da tsari na musamman a bangaren aikin jarida ta kafafen sadarwa na zamani, yawan mutane da ke bibiyarmu da kuma sakonnin da muke samu a kullum shaida ne ga yada aka karbe mu, yana kuma nuna irin kokarinmu a wannan fagen.
“Mun samar da shirye-shirye da dama, muna ci gaba da inganta su tare da tsayuwa a kan bayar da sahihan labarai. Za mu nisanci dukkan nau’in labarun kazon kurege, za kuma mu tabbatar da kowa ya samu hakkin fadar albarkacin bakinsa a dukkan lokaci,” in ji shi.

Mista Amodu ya kuma bayana cewa, bayan shirye-shirye ta Podcast, Kamfanin LEADERSHIP Group Limited, na kuma jagorantar buga Jaridar LEADERSHIP Daily, LEADERSHIP Weekend, LEADERSHIP Sunday, LEADERSHIP Hausa da kuma National Economy.

Daga cikin manya manyan shirye shiryen da ake gabatarwa a dakin watsa shirye-shiryen na LAST WORD akwai shirin sashashin Hausa na LEADERSHIP mai lakabin ‘BARKA DA HANTSI NIJERIYA’ wanda ake gabatarwa da misalin karfe 9 na safe daga Litinin har zuwa Juma’a kai-tsaye ta kafofin Facebook a “Leadership Hausa”, YouTube a “Leadership Hausa”, sai kafar Twitter a “@Leadershiphausa”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Muna Da Hujjojin Magudi A Zaben Fid Da Gwanin PDP Na Kaduna Ta Tsakiya – Lauya

Next Post

Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

Related

Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

3 days ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

3 days ago
Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu
Rahotonni

Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

4 days ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

1 week ago
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

1 week ago
Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

2 weeks ago
Next Post
Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

September 2, 2025
Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

September 1, 2025
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

September 1, 2025
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

September 1, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

September 1, 2025
Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

September 1, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

September 1, 2025
Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.