• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitoci 10,000 Kacal Suka Rage A Nijeriya – NARD

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Likitoci 10,000 Kacal Suka Rage A Nijeriya – NARD
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar likitocin Nijeriya (NARD) ta bayyana cewa yawan likitocin kasar nan suna raguwa a kullun, inda ta ce a halin yanzu likitoci 10,000 kacal suka rage.

Shugaban kungiyar NARD, Dakta Emeka Orji shi ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Litinin da ta gabata.

  • Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace
  • Buhari Ne Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Kangin Talauci — Gwamnoni

A cewar Orji, sama da likitoci 100 suke barin kasar a duk wata wajen neman aiki mai kwabi a kasashen ketare.

Ya ce, “Na sani a halin yanzu muna da likitoci 24,000 ciki har da kwararu da likitocin gida da sauran ma’aikatan lafiya. A cikin likitoci 80,000 da aka yi wa rajista, kashi 64 ba sa gudanar da aikin, wasu sun fice daga kasar, yayin da wasu sun yi ritaya, wasu sun sauya aiki, wasu kuma sun mutu.

“Likitocin gida da muke amfani da su guda 16,000 a baya, amma a yanzu muna da 9,000 zuwa 10,000. Ba za mu iya tatance yawan likitocin ba a kullum, saboda ficewa da suke yi. Saboda haka, a yanzu haka muna da likitoci a tsakanin 9,000 zuwa 10,000 a fadin kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

“A jimlace, muna da likitoci 24,000 ciki har da kwararu da likitocin gida da ma’aikatan lafiya. Kungiyar kula da lafiya ta duniya ta bayar da shawarar cewa ilita daya ya dunga duba majinya ta 600, amma a halin yanzu a Nijeriya, likita daya yana duba marasa lafiya guda 10,000.”

Shugaban NARD ya kara da cewa babban matsalar da ta kawo ficewar likitocin shi ne, rashin ba su hakkokinsu da rashin samun walwala da kuma rashin tsarin samar da gidajensu.

“Muna fuskantar rashin kyawun yanayin wurin aiki a kasar nan, idan gwamnati tana son ma’aikata su gudanar da aiki yadda ya kamata, to dole ne ta inganta wuraren aiki. Idan ana bukatar bangaren lafiya ya kasance da ransa, to dole kowa ya saka hannu cikin lamarin.

“A wannan shekarar tsakanin watannin Janairu zuwa Agusta, mun rasa sama da likitoci 800, lokacin da muka tambaye su dalilin ficewarsu, kashi 80 sun bayyana cewa saboda rashin biyansu hakkokinsu da kuma rashin kyawon wurin zama,” in ji Orji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LikitociNARD
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Za Mu Kula Da Yara Lokacin Sanyi

Next Post

Makarantar Firamare Mai Malamai 2 Kacal Da Adadin Dalibai 544 A Jihar Yobe

Related

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar
Manyan Labarai

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

9 hours ago
Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

1 day ago
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya
Manyan Labarai

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

2 days ago
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

2 days ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

3 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

3 days ago
Next Post
Makarantar Firamare Mai Malamai 2 Kacal Da Adadin Dalibai 544 A Jihar Yobe

Makarantar Firamare Mai Malamai 2 Kacal Da Adadin Dalibai 544 A Jihar Yobe

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

May 11, 2025
Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

May 11, 2025
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

May 11, 2025
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

May 11, 2025
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

May 11, 2025
Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

May 11, 2025
Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

May 11, 2025
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.