ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitoci 10,000 Kacal Suka Rage A Nijeriya – NARD

by Leadership Hausa
4 years ago
Likitoci

Kungiyar likitocin Nijeriya (NARD) ta bayyana cewa yawan likitocin kasar nan suna raguwa a kullun, inda ta ce a halin yanzu likitoci 10,000 kacal suka rage.

Shugaban kungiyar NARD, Dakta Emeka Orji shi ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Litinin da ta gabata.

  • Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace
  • Buhari Ne Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Kangin Talauci — Gwamnoni

A cewar Orji, sama da likitoci 100 suke barin kasar a duk wata wajen neman aiki mai kwabi a kasashen ketare.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Na sani a halin yanzu muna da likitoci 24,000 ciki har da kwararu da likitocin gida da sauran ma’aikatan lafiya. A cikin likitoci 80,000 da aka yi wa rajista, kashi 64 ba sa gudanar da aikin, wasu sun fice daga kasar, yayin da wasu sun yi ritaya, wasu sun sauya aiki, wasu kuma sun mutu.

“Likitocin gida da muke amfani da su guda 16,000 a baya, amma a yanzu muna da 9,000 zuwa 10,000. Ba za mu iya tatance yawan likitocin ba a kullum, saboda ficewa da suke yi. Saboda haka, a yanzu haka muna da likitoci a tsakanin 9,000 zuwa 10,000 a fadin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

“A jimlace, muna da likitoci 24,000 ciki har da kwararu da likitocin gida da ma’aikatan lafiya. Kungiyar kula da lafiya ta duniya ta bayar da shawarar cewa ilita daya ya dunga duba majinya ta 600, amma a halin yanzu a Nijeriya, likita daya yana duba marasa lafiya guda 10,000.”

Shugaban NARD ya kara da cewa babban matsalar da ta kawo ficewar likitocin shi ne, rashin ba su hakkokinsu da rashin samun walwala da kuma rashin tsarin samar da gidajensu.

“Muna fuskantar rashin kyawun yanayin wurin aiki a kasar nan, idan gwamnati tana son ma’aikata su gudanar da aiki yadda ya kamata, to dole ne ta inganta wuraren aiki. Idan ana bukatar bangaren lafiya ya kasance da ransa, to dole kowa ya saka hannu cikin lamarin.

“A wannan shekarar tsakanin watannin Janairu zuwa Agusta, mun rasa sama da likitoci 800, lokacin da muka tambaye su dalilin ficewarsu, kashi 80 sun bayyana cewa saboda rashin biyansu hakkokinsu da kuma rashin kyawon wurin zama,” in ji Orji.

Likitoci
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
Manyan Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Next Post
Makarantar Firamare Mai Malamai 2 Kacal Da Adadin Dalibai 544 A Jihar Yobe

Makarantar Firamare Mai Malamai 2 Kacal Da Adadin Dalibai 544 A Jihar Yobe

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.