• Leadership Hausa
Monday, February 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Makarantar Firamare Mai Malamai 2 Kacal Da Adadin Dalibai 544 A Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
2 months ago
in Labarai
0
Makarantar Firamare Mai Malamai 2 Kacal Da Adadin Dalibai 544 A Jihar Yobe

Duk da yawan ikirarin da gwamnatin jihar Yobe ta sha yi wajen inganta harkokin ilimi, kafa kwamitin sake farfado da fannin, wakilinmu ya gano wata makarantar firamare a kauyen Ngelshengele da ke karamar hukumar Fune a jihar; mai malamai biyu kacal tare da adadin dalibai 544 a ajujuwan makarantar.

LEADERSHIP Hausa ta jiyo ta bakin shugaban makarantar (Headmaster) Malam Sa’id Wakil, inda ya koka dangane da rashin malamai a makarantar, kana kuma al’amarin da ya ce yana daya daga cikin manyan kalubalen da Firamare ta Ngelshengele ke fuskanta. Inda ya ce malamai biyu ne kawai a makarantar.

  • Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace

“Akwai wani malami daya wanda aka turo shi zuwa wannan makarantar, amma mun gano cewa dalibi ne daga Gashuwa. Sannan a gaskiya ban ma san shi ba, amma ko shakka babu zuwan sa zai taimaka.” inji shi.

Malam Sa’id ya ce, “Baya ga rashin malamai, kusan dukkan ajujuwan wannan makaranta na bukatar gyara. Kamar yadda kuke gani, duk sun lalace.”

Bugu da kari kuma, ya ce duk da an gyara wasu azuzuwan ne ta tallafin bankin duniya da kwamitin kula da makarantu (SBMC). Ya kara da cewa, kimanin N500,000 ne aka tara domin gyara wasu azuzuwan da daliban ke daukar darasi a halin yanzu.

Labarai Masu Nasaba

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

A hannu guda kuma, da yake ci gaba da tsokaci kan kalubalen da Firamaren ke fuskanta, shugaban makarantar ya ce a lokacin damina, da zarar sun ga alamar hadari ya taso, sai su tura daliban gida, su kwashe kayan karatu; kujeru da makamantan su zuwa gidan Hakimin kauye domin kaucewa faruwar hatsari ga daliban daga ruwan sama da iska su halaka su.

Ya kara da cewa, wadannan matsalolin sune suke tilastawa yara da dama barin makaranta a kauyukan, al’amarin da ya katangance yaran daga yancin samun karatu.

A nashi bangaren, Kwamishina a Ma’aikatar Ilimi a matakin farko a jihar Yobe, Dokta Muhammad Sani Idrissa, ya ce “To, gwamnatinmu ta gaji halin kuncin da fannin ilimi ke ciki, musamman yanayin da wasu makarantun ke ciki. Mun fahimci cewa akalla makarantun firamare da sakandare 1,300 ne ke bukatar gyara. Amma cikin kankanin lokaci mun gyara akalla guda 300 kuma muna fatan nan gaba kadan makarantu 1000 za su kasance a cikin ayyukanmu na gyara da muke yi, kuma Makarantar Firamare ta Ngelshengele za ta kasance a cikinsu,” inji shi.

Previous Post

Likitoci 10,000 Kacal Suka Rage A Nijeriya – NARD

Next Post

Aisha Buhari: Aminu Ya Nemi Yafiyar Uwargidan Shugaban Kasa Kan Shaguben Da Ya Yi Mata

Related

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri
Rahotonni

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

4 hours ago
Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?
Labarai

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

6 hours ago
NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

7 hours ago
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta
Kotu Da Ɗansanda

Ya Kashe Makocinsa Don Ya Haske Idon Mahaifiyarsa Da Cocila

10 hours ago
Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Tir Da Kisan Fulani 40 A Jihar Nasarawa
Labarai

Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Tir Da Kisan Fulani 40 A Jihar Nasarawa

12 hours ago
Sojoji Sun Kama Mutum 116 Da Ke Yin Laifuka Daban-daban A Legas
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Kama Mutum 116 Da Ke Yin Laifuka Daban-daban A Legas

13 hours ago
Next Post
Aisha Buhari: “Ko A Sako Dalibin Da Aka Kama Ko Mu Fara Zanga-Zanga” – Kungiyar Daliban Nijeriya

Aisha Buhari: Aminu Ya Nemi Yafiyar Uwargidan Shugaban Kasa Kan Shaguben Da Ya Yi Mata

LABARAI MASU NASABA

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

February 5, 2023
Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

February 5, 2023
Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

February 5, 2023
Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

February 5, 2023
Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

February 5, 2023
Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

February 5, 2023
An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

February 5, 2023
NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

February 5, 2023
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta

Ya Kashe Makocinsa Don Ya Haske Idon Mahaifiyarsa Da Cocila

February 5, 2023
Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

February 5, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.