ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makarantar Firamare Mai Malamai 2 Kacal Da Adadin Dalibai 544 A Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
4 years ago
Yobe

Duk da yawan ikirarin da gwamnatin jihar Yobe ta sha yi wajen inganta harkokin ilimi, kafa kwamitin sake farfado da fannin, wakilinmu ya gano wata makarantar firamare a kauyen Ngelshengele da ke karamar hukumar Fune a jihar; mai malamai biyu kacal tare da adadin dalibai 544 a ajujuwan makarantar.

LEADERSHIP Hausa ta jiyo ta bakin shugaban makarantar (Headmaster) Malam Sa’id Wakil, inda ya koka dangane da rashin malamai a makarantar, kana kuma al’amarin da ya ce yana daya daga cikin manyan kalubalen da Firamare ta Ngelshengele ke fuskanta. Inda ya ce malamai biyu ne kawai a makarantar.

  • Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace

“Akwai wani malami daya wanda aka turo shi zuwa wannan makarantar, amma mun gano cewa dalibi ne daga Gashuwa. Sannan a gaskiya ban ma san shi ba, amma ko shakka babu zuwan sa zai taimaka.” inji shi.

ADVERTISEMENT

Malam Sa’id ya ce, “Baya ga rashin malamai, kusan dukkan ajujuwan wannan makaranta na bukatar gyara. Kamar yadda kuke gani, duk sun lalace.”

Bugu da kari kuma, ya ce duk da an gyara wasu azuzuwan ne ta tallafin bankin duniya da kwamitin kula da makarantu (SBMC). Ya kara da cewa, kimanin N500,000 ne aka tara domin gyara wasu azuzuwan da daliban ke daukar darasi a halin yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

A hannu guda kuma, da yake ci gaba da tsokaci kan kalubalen da Firamaren ke fuskanta, shugaban makarantar ya ce a lokacin damina, da zarar sun ga alamar hadari ya taso, sai su tura daliban gida, su kwashe kayan karatu; kujeru da makamantan su zuwa gidan Hakimin kauye domin kaucewa faruwar hatsari ga daliban daga ruwan sama da iska su halaka su.

Ya kara da cewa, wadannan matsalolin sune suke tilastawa yara da dama barin makaranta a kauyukan, al’amarin da ya katangance yaran daga yancin samun karatu.

A nashi bangaren, Kwamishina a Ma’aikatar Ilimi a matakin farko a jihar Yobe, Dokta Muhammad Sani Idrissa, ya ce “To, gwamnatinmu ta gaji halin kuncin da fannin ilimi ke ciki, musamman yanayin da wasu makarantun ke ciki. Mun fahimci cewa akalla makarantun firamare da sakandare 1,300 ne ke bukatar gyara. Amma cikin kankanin lokaci mun gyara akalla guda 300 kuma muna fatan nan gaba kadan makarantu 1000 za su kasance a cikin ayyukanmu na gyara da muke yi, kuma Makarantar Firamare ta Ngelshengele za ta kasance a cikinsu,” inji shi.

Yobe
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Next Post
Aisha Buhari: “Ko A Sako Dalibin Da Aka Kama Ko Mu Fara Zanga-Zanga” – Kungiyar Daliban Nijeriya

Aisha Buhari: Aminu Ya Nemi Yafiyar Uwargidan Shugaban Kasa Kan Shaguben Da Ya Yi Mata

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.