ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makarantar Firamare Mai Malamai 2 Kacal Da Adadin Dalibai 544 A Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
4 years ago
Yobe

Duk da yawan ikirarin da gwamnatin jihar Yobe ta sha yi wajen inganta harkokin ilimi, kafa kwamitin sake farfado da fannin, wakilinmu ya gano wata makarantar firamare a kauyen Ngelshengele da ke karamar hukumar Fune a jihar; mai malamai biyu kacal tare da adadin dalibai 544 a ajujuwan makarantar.

LEADERSHIP Hausa ta jiyo ta bakin shugaban makarantar (Headmaster) Malam Sa’id Wakil, inda ya koka dangane da rashin malamai a makarantar, kana kuma al’amarin da ya ce yana daya daga cikin manyan kalubalen da Firamare ta Ngelshengele ke fuskanta. Inda ya ce malamai biyu ne kawai a makarantar.

  • Celestine Babayaro Ya Sake Bayyana Bayan Ya Bace

“Akwai wani malami daya wanda aka turo shi zuwa wannan makarantar, amma mun gano cewa dalibi ne daga Gashuwa. Sannan a gaskiya ban ma san shi ba, amma ko shakka babu zuwan sa zai taimaka.” inji shi.

ADVERTISEMENT

Malam Sa’id ya ce, “Baya ga rashin malamai, kusan dukkan ajujuwan wannan makaranta na bukatar gyara. Kamar yadda kuke gani, duk sun lalace.”

Bugu da kari kuma, ya ce duk da an gyara wasu azuzuwan ne ta tallafin bankin duniya da kwamitin kula da makarantu (SBMC). Ya kara da cewa, kimanin N500,000 ne aka tara domin gyara wasu azuzuwan da daliban ke daukar darasi a halin yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

A hannu guda kuma, da yake ci gaba da tsokaci kan kalubalen da Firamaren ke fuskanta, shugaban makarantar ya ce a lokacin damina, da zarar sun ga alamar hadari ya taso, sai su tura daliban gida, su kwashe kayan karatu; kujeru da makamantan su zuwa gidan Hakimin kauye domin kaucewa faruwar hatsari ga daliban daga ruwan sama da iska su halaka su.

Ya kara da cewa, wadannan matsalolin sune suke tilastawa yara da dama barin makaranta a kauyukan, al’amarin da ya katangance yaran daga yancin samun karatu.

A nashi bangaren, Kwamishina a Ma’aikatar Ilimi a matakin farko a jihar Yobe, Dokta Muhammad Sani Idrissa, ya ce “To, gwamnatinmu ta gaji halin kuncin da fannin ilimi ke ciki, musamman yanayin da wasu makarantun ke ciki. Mun fahimci cewa akalla makarantun firamare da sakandare 1,300 ne ke bukatar gyara. Amma cikin kankanin lokaci mun gyara akalla guda 300 kuma muna fatan nan gaba kadan makarantu 1000 za su kasance a cikin ayyukanmu na gyara da muke yi, kuma Makarantar Firamare ta Ngelshengele za ta kasance a cikinsu,” inji shi.

Yobe
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Aisha Buhari: “Ko A Sako Dalibin Da Aka Kama Ko Mu Fara Zanga-Zanga” – Kungiyar Daliban Nijeriya

Aisha Buhari: Aminu Ya Nemi Yafiyar Uwargidan Shugaban Kasa Kan Shaguben Da Ya Yi Mata

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.