ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatan Shari’a Sun Fara Yajin Aiki Kan Bashin Albashi Da Kuɗin Hutu A Kogi

by Abubakar Sulaiman
2 weeks ago
Kogi

LABARAI MASU NASABA

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Ma’aikatan shari’a a Jihar Kogi ƙarƙashin ƙungiyar JUSUN sun shiga yajin aikin sai baba ta gani sakamakon gazar gwamnati na cika alƙawarin biyan bashin watan Oktoba 2024 da kuɗin hutun shekarar 2025. A cikin sanarwar da shugaban JUSUN, Emmanuel Waniko, da sakatare, Sule Suberu, suka fitar, ƙungiyar ta ce an shiga yajin aikin ne bayan jinkirin da gwamnati ta yi duk da alkawurran da ta ɗauka tun lokacin da aka dakatar da wani yajin aikin da ya gabata.

JUSUN ta bayyana cewa Gwamna Usman Ododo ya tabbatar da amincewa da biyan kuɗaɗen, amma ba a ga wani mataki ba na aiwatar da hakan duk da haƙurin da ma’aikata suka nuna. Kungiyar ta ce dole ne ta ɗauki wannan mataki domin kare muradun membobinta da ke fama da matsin tattalin arziki sakamakon biyan da ya tsaya.

  • Mutum 4 Sun Mutu Yayin Da ’Yan Bindiga Sake Kai Hari Kogi
  • Gwamnatin Kogi Ta Ƙaryata Rahoton Sace Ɗalibai A Jiharta

Sanarwar ta bayyana cewa daga ranar Alhamis, 4 ga Disamba 2025, dukkan ma’aikatan shari’a a jihar su dakatar da aiki gaba ɗaya, tare da gargadin cewa ba a yarda wani ya shiga ko ya gudanar da wani aiki na hukuma ba har sai an biya kuɗaɗen da ake binsu. Ƙungiyar ta jaddada cewa har sai an biya bashin watan Oktoba 2024 da kuɗin hutun 2025, babu komawa bakin aiki.

ADVERTISEMENT

JUSUN ta yabawa membobinta bisa jajircewa da haɗin kai, sannan ta bukaci su ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen ganin an biya haƙƙinsu. A halin yanzu dai sashen shari’a na jihar ya tsaya cik, lamarin da ka iya kawo tsaiko ga ayyukan kotuna idan gwamnati ba ta gaggauta ɗaukar mataki ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Next Post
Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi

Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.