ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahara Sun Sake Kai Hari, Sun Sace Dan Sarkin Bungudu Da Wasu Mutane 6 A Zamfara

by Muhammad
2 years ago
Zamfara

A safiyar ranar Litinin wasu ‘yan bindiga suka kai hari hedikwatar karamar hukumar Bungudu ta jihar Zamfara, inda suka kashe mutum daya tare da yin awon gaba da wasu bakwai.

LEADERSHIP ta rawaito cewa a makon da ya gabata ‘yan bindigar sun kai hari a ofishin ‘yan sanda na Bungudu inda suka kashe dan sanda daya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Karbe Ikon Kauyuka 400 A Zamfara -Masani
  • ‘Yansanda Sun Dakile Harin ‘Yan Bindiga A Masallacin Juma’a A Zamfara

Wani mazaunin garin Bungudu mai suna, Ishaq Bungudu, ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun afkawa garin da muggan makamai inda suka yi ta harbe-harbe tare da kashe wani mutum.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda ya shaida, ya ce, an yi garkuwa da wasu mutane bakwai da suka hada da dan Sarkin Bungudu, Abdulrahman Hassan, da kuma tsohon jami’in tsare-tsare na asusun bunkasa noma na kasa da kasa (IFAD), Abubakar S/Fada Bungudu.

Ishaq ya koka kan yawaitar hare-haren da ‘yan bindiga suka kai hedikwatar karamar hukumar a tsukin nan, duk da cewa ita ce karamar hukuma mafi kusa da Gusau babban birnin jihar.

LABARAI MASU NASABA

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Ishaq ya bukaci gwamnan jihar, Dauda Lawal, da ya yi kokarin magance kalubalen rashin tsaro da ya addabi jihar.

“Kusan kullum ana kai mana hari, duk da cewa muna kusa da Gusau babban birnin jihar, ba mu san me ke faruwa ba, gwamnati ba ta cewa komai, shi (gwamna) ma ba shi da mai taimaka wa harkar tsaro tun da aka rantsar da shi.

“Ya kamata ya nada mai taimaka wa gwamna ta fuskar tsaro domin mutane su san wanda za su kira a lokacin suka samu kansu yayin da aka afka musu, ba mu ma san abin da za mu yi ba a yanzu, ‘yan fashi za su shiga tsakiyar gari su kashe mutane, abin ya tayar da hankali matuka.” Cewar Ishaq.

LEADERSHIP ta rawaito cewa hedikwatar karamar hukumar Bungudu na da tazarar kilomita 21 zuwa babban birnin jihar.

Idan dai ba a manta ba an kashe ‘yan sanda hudu a watan da ya gabata a karamar hukumar, sannan an kashe wani dan sanda a kwanakin baya a wasu hare-hare da aka kai yankin.

Mun yi kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, ASP Yazid Abubakar, sai dai bamu same shi ba, domin bai amsa kiran waya da aka yi masa ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa
Manyan Labarai

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN
Manyan Labarai

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Next Post
Kano Pillars Ta Dauki Sabon Dan Wasa Daga Rivers United

Kano Pillars Ta Dauki Sabon Dan Wasa Daga Rivers United

LABARAI MASU NASABA

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.