• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahara Sun Sake Kai Hari, Sun Sace Dan Sarkin Bungudu Da Wasu Mutane 6 A Zamfara

by Muhammad
2 years ago
Zamfara

A safiyar ranar Litinin wasu ‘yan bindiga suka kai hari hedikwatar karamar hukumar Bungudu ta jihar Zamfara, inda suka kashe mutum daya tare da yin awon gaba da wasu bakwai.

LEADERSHIP ta rawaito cewa a makon da ya gabata ‘yan bindigar sun kai hari a ofishin ‘yan sanda na Bungudu inda suka kashe dan sanda daya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Karbe Ikon Kauyuka 400 A Zamfara -Masani
  • ‘Yansanda Sun Dakile Harin ‘Yan Bindiga A Masallacin Juma’a A Zamfara

Wani mazaunin garin Bungudu mai suna, Ishaq Bungudu, ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun afkawa garin da muggan makamai inda suka yi ta harbe-harbe tare da kashe wani mutum.

Kamar yadda ya shaida, ya ce, an yi garkuwa da wasu mutane bakwai da suka hada da dan Sarkin Bungudu, Abdulrahman Hassan, da kuma tsohon jami’in tsare-tsare na asusun bunkasa noma na kasa da kasa (IFAD), Abubakar S/Fada Bungudu.

Ishaq ya koka kan yawaitar hare-haren da ‘yan bindiga suka kai hedikwatar karamar hukumar a tsukin nan, duk da cewa ita ce karamar hukuma mafi kusa da Gusau babban birnin jihar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ishaq ya bukaci gwamnan jihar, Dauda Lawal, da ya yi kokarin magance kalubalen rashin tsaro da ya addabi jihar.

“Kusan kullum ana kai mana hari, duk da cewa muna kusa da Gusau babban birnin jihar, ba mu san me ke faruwa ba, gwamnati ba ta cewa komai, shi (gwamna) ma ba shi da mai taimaka wa harkar tsaro tun da aka rantsar da shi.

“Ya kamata ya nada mai taimaka wa gwamna ta fuskar tsaro domin mutane su san wanda za su kira a lokacin suka samu kansu yayin da aka afka musu, ba mu ma san abin da za mu yi ba a yanzu, ‘yan fashi za su shiga tsakiyar gari su kashe mutane, abin ya tayar da hankali matuka.” Cewar Ishaq.

LEADERSHIP ta rawaito cewa hedikwatar karamar hukumar Bungudu na da tazarar kilomita 21 zuwa babban birnin jihar.

Idan dai ba a manta ba an kashe ‘yan sanda hudu a watan da ya gabata a karamar hukumar, sannan an kashe wani dan sanda a kwanakin baya a wasu hare-hare da aka kai yankin.

Mun yi kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, ASP Yazid Abubakar, sai dai bamu same shi ba, domin bai amsa kiran waya da aka yi masa ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
Manyan Labarai

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Next Post
Kano Pillars Ta Dauki Sabon Dan Wasa Daga Rivers United

Kano Pillars Ta Dauki Sabon Dan Wasa Daga Rivers United

LABARAI MASU NASABA

Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

October 20, 2025
Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

October 20, 2025
Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.