ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahara Sun Sake Kai Hari, Sun Sace Dan Sarkin Bungudu Da Wasu Mutane 6 A Zamfara

by Muhammad
3 years ago
Zamfara

A safiyar ranar Litinin wasu ‘yan bindiga suka kai hari hedikwatar karamar hukumar Bungudu ta jihar Zamfara, inda suka kashe mutum daya tare da yin awon gaba da wasu bakwai.

LEADERSHIP ta rawaito cewa a makon da ya gabata ‘yan bindigar sun kai hari a ofishin ‘yan sanda na Bungudu inda suka kashe dan sanda daya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Karbe Ikon Kauyuka 400 A Zamfara -Masani
  • ‘Yansanda Sun Dakile Harin ‘Yan Bindiga A Masallacin Juma’a A Zamfara

Wani mazaunin garin Bungudu mai suna, Ishaq Bungudu, ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun afkawa garin da muggan makamai inda suka yi ta harbe-harbe tare da kashe wani mutum.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda ya shaida, ya ce, an yi garkuwa da wasu mutane bakwai da suka hada da dan Sarkin Bungudu, Abdulrahman Hassan, da kuma tsohon jami’in tsare-tsare na asusun bunkasa noma na kasa da kasa (IFAD), Abubakar S/Fada Bungudu.

Ishaq ya koka kan yawaitar hare-haren da ‘yan bindiga suka kai hedikwatar karamar hukumar a tsukin nan, duk da cewa ita ce karamar hukuma mafi kusa da Gusau babban birnin jihar.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Ishaq ya bukaci gwamnan jihar, Dauda Lawal, da ya yi kokarin magance kalubalen rashin tsaro da ya addabi jihar.

“Kusan kullum ana kai mana hari, duk da cewa muna kusa da Gusau babban birnin jihar, ba mu san me ke faruwa ba, gwamnati ba ta cewa komai, shi (gwamna) ma ba shi da mai taimaka wa harkar tsaro tun da aka rantsar da shi.

“Ya kamata ya nada mai taimaka wa gwamna ta fuskar tsaro domin mutane su san wanda za su kira a lokacin suka samu kansu yayin da aka afka musu, ba mu ma san abin da za mu yi ba a yanzu, ‘yan fashi za su shiga tsakiyar gari su kashe mutane, abin ya tayar da hankali matuka.” Cewar Ishaq.

LEADERSHIP ta rawaito cewa hedikwatar karamar hukumar Bungudu na da tazarar kilomita 21 zuwa babban birnin jihar.

Idan dai ba a manta ba an kashe ‘yan sanda hudu a watan da ya gabata a karamar hukumar, sannan an kashe wani dan sanda a kwanakin baya a wasu hare-hare da aka kai yankin.

Mun yi kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, ASP Yazid Abubakar, sai dai bamu same shi ba, domin bai amsa kiran waya da aka yi masa ba.

Zamfara
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Kano Pillars Ta Dauki Sabon Dan Wasa Daga Rivers United

Kano Pillars Ta Dauki Sabon Dan Wasa Daga Rivers United

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.