• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mai Martaba Sarkin Hadeja Zai Cika Shekara 20 Kan Karaga

by Mika'il Tsoho
3 years ago
in Rahotonni
0
hadeja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 14 ga watan Satumba na kowacce shekara ta kasance wata rana ta musamman ga kafatanin al’ummar Masarautar Hadeja, sakamakon a ranar ne da Mai Martaba Sarkin Hadeja Dakta Adamu Abubakar Maje yake cika shekara 20 a kan karagar mulki a matsayin Sarkin Hadeja (a cikin jerin sarakunan Fulani) na 16 a Masarautar.

Mai Martaba Sarkin Hadeja kuma shugaban majalisar Sarakunan Jihar Jigawa, wadda duk duniya ta yi masa shaida wajen hidimta wa addini da al’ummarsa musamman masu karamin karfi, mata da kananan yara da marayu, ya kasance Sarki Mai ilimin addini da na zamani.

  • Masarautar Mubi Da Kyakkyawan Shugabancin Sarki Alhaji Abubakar Isa Ahmadu

Haka kuma cikin shekara ashirin da Sarkin ya share kan karagar mulkin Masarautar, an sami gwaggwaban ci gaba a fannonin rayuwa a yankin, wadda hakan ya sanya Masarautar ta Hadeja ta zarce sa a akowanne fanni na rayuwa.

Masarautar Hadeja ta kasance daya daga cikin masarautu biyar masu dumbin tarihi a jihar Jigawa da ma kasar Hausa baki daya, haka kuma Sarkin na Hadeja shi ne a matsayin jagora ga dukkanin sauran masarautun da ke fadin jihar.

Yankin na Hadeja wadda ya kunshi manyan garuruwa masu tarihi a kasar Hausa, na da kananan hukumomi guda takwas da suka hada da Hadeja, Kafin Hausa, Auyo, Malam-madori, Kaugama, Kiri-kasamma, Birniwa da karamar hukumar Guri.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Yankin Hadeja wadda ke Gabashin jihar ta Jigawa, Allah ya albarkace shi da masu ilimin addini da na zamani, ga kasar noma da kasuwanci, manyan ma’aikata a matakin kasa da jiha baki daya, wadda hakan ya sanya yankin bunkasa fiye da kowanne yanki a jihar.

Dangane da kafuwar masarautar kuwa, tarihi ya nuna cewa, yankin na Hadeja na da dimbin tarihi tun Kafin zuwan turawan mulkin mallaka domin kuwa ko a wancan lokaci, Hadeja Masarauta ce mai kunshe da Jarumai, Attajirai da Masana illimi.

Tarihi ya bayyana cewa tun kimanin shekarar 11,000, Habe ke mulki a yankin Garun-Gabas wadda ke karkashin karamar hukumar Malam-madori a yanzu, kuma sun yi fitattu kuma jaruman Sarakuna masu yawa wadanda suka hada da Sarki Kankarau, Asawa, Mamman Bako, Kawu, Baude, Musa da Kuma Abubakar.

Haka kuma tarihi ya bayyana cewa, a shekarar 1808 ne Fulani suka fara karbe mulki daga Habe a masarautar ta Hadeja kuma suka ci gaba da yi har zuwa wannan lokaci.

“A Lokacin Sarkin Hadejia na Habe Abubakar ne Fulani suka zo kasar Hadejia, a karkashin jagorancin Ardo Abdure dan Jamdoji, kuma Sarkin Habe Abubakar shi ne ya basu wurin zama, kana a zamanin Sarkin Fulani Sambo suka dawo Inda fadar Hadejia take yanzu, kafin daga bisa su kwaci mulki a hannun Sarakunan Habe a karkashin tutar Jihadin Shehu Usmanu Danfodiyo”.

Sarakunan Fulani a masarautar ta Hadeja sun hada da Sarki Umaru Dan Ardo Abdure 1805 – 1808, Sarki Mamman Kankiya Dan Umaru 1808 – 1808, Sarki Sambo Dan Ardo Abdure 1808 -1845, sai kuma Sarki Garko Gambo Dan Sambo 1845 – 1847, Sarki Abdulkadir Dan Sambo 1847 – 1848, Sarki Sambo Dan Ardo Abdure 1848 – 1848 (Hawa na biyu).
Sai Kuma Sarki Buhari Dan Sambo 1848 – 1850 (hawan farko), Sarki Ahmadu Dan Sambo 1850 – 1851, Sarki Buhari Dan Sambo 1851 – 1863 (Hawa na biyu), Sarki Umaru Dan Buhari 1863 – 1865, Sarki Haruna Bubba Dan Sambo 1865 – 1885, Sarki Muhammadu Maishahada Dan Haru Bubba 1885 – 1906.

Sauran Sarakunan sun hada da Sarki Haru Mai Karamba Dan Muhammadu 1906 – 1909, Sarki Abdulkadir Dan Haru Mai Karamba 1909 – 1925, Sarki Usman Dan Haru Mai Karamba 1925 – 1950, Sarki Haruna Dan Abdulkadir 1950 – 1985, Sarki Abubakar Maje Dan Haruna 1985 – 2002, sai kuma Mai Martaba Sarki Dakta Adamu Dan Abubakar Maje wanda shi ne a kan karagar mulkin Masarautar Hadeja har zuwa yanzu.

Mai martaba Sarki Dakta Adamu Abubakar Maje ya kasance Sarki na 16 a jerin Sarakunan Fulani a Hadeja, kuma ya zama Sarki a ranar 14 ga watan Satumbar shekarar 2002, bayan rasuwar mahaifinsa a ranar 11 ga watan na Satumba.

Kafin rasuwar mahaifinsa ya nada shi a matsayin IYAN HADEJA na farko, a ranar 3 ga watan Janairun shekarar 1999 yadda daga bisani ranar Laraba 11 ga watan Satumba na shekarar 2002 kuma Allah ya yi wa mahaifin nasa rasuwa.

Sannan a ranar 14 ga watan Satumbar kamar yadda al’adar Masarautar ta amince a nada sabon Sarki Kafin kwanaki uku da rasuwar wadda ke karagar. Don haka majalisar Sarki suka nada shi a matsayin sabon Sarkin Hadeja na 16 bayan amincewar gwamnatin wannan lokaci.

Haka kuma an yi bikin bashi Sanda a ranar 29 ga watan Maris 2003, wadda gwamnan jihar Jigawa a wannan lokaci Alhaji Ibrahim Saminu Turaki ya jagoranta kuma aka gudanar a filin wasanni na Hadeja.

Mai Martaba Sarki bayan an bashi Sandar jagorancin kasar Hadejia a karkashin tutar Shehu Usman Dan Fodiyo, yadda daga nan kuma shagulgulan biki suka fara.

Mai Martaba Sarki ya gudanar da kayatattun Hawa guda uku tare da gudanar da addu’o’i da karatun Alkur’ani a Masarautar.

Shi dai Mai Martaba Sarkin Hadeja an haife shi ne ranar 15 ga watan Oktoba na shekar 1960, a cikin birnin Hadejia a tsohuwar Jihar Kano.

Mai Martaba Sarki ya fara karatun firamare a shekar 1967 zuwa 1972 a Makarantar Abdulkadir Primary school Hadeja. Daga bisani ya shiga Makarantar Sakandire ta Garin Ikot Ekpene Cross-riber a shekarar 1973 zuwa1976, sannan ya koma makarantar Sakandire ta Danbatta a shekarar 1976-1979.

Mai Martaba Sarki ya samu nasarar shiga Makarantar Gaba da Secondary ta school of Rural and social science da ke Rano a Jihar Kano a shekarar 1981-1982, da kuma 1983-1985.

Mai Martaba Sarki ya fara aikin Gwamnati a tsohuwar Jihar Kano a ma’aikatar walwalar al’umma, a shekarar 1982-1988, sannan ya koma hukumar jindadi da walwalar Alhazai ta jihar Kano a shekarar 1988-1991.

Bayan da aka kirkiro Jihar Jigawa Mai Martaba Sarkin Hadejia ya koma hukumar jindadi da walwalar Alhazai ta jihar Jigawa a shekarar 1991-1998. Sannan ya koma Ma’aikatar Kananan Hukumomi ta jiha a shekarar 1998-1999.

A wannan shekarar ne Mai Martaba Sarkin Hadejia Dakta Abubakar Maje Haruna ya nadashi sarautar IYAN HADEJA kuma dan majalissar Sarki kafin daga bisani kuma a nada shi a matsayin Sarkin Hadeja na 16.

Daga karshe jaridar LEADERSHIP Hausa da ma’aikatanta na taya Mai Martaba Sarki murna tare da fatan Allah ya kara wa Sarki lafiya da nisan kwana masu albarka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda ‘Yan Kasuwar Kwari Ke Tafka Asara Saboda Ambaliyar Ruwa A Kano

Next Post

Sojoji Sun Ceto Wasu Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Birnin Gwari

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

1 week ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

2 weeks ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

2 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

2 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
Sojoji Sun Ceto Wasu Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Birnin Gwari

Sojoji Sun Ceto Wasu Da 'Yan Bindiga Suka Sace A Birnin Gwari

LABARAI MASU NASABA

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

August 5, 2025
Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

August 5, 2025
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama ÆŠalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama ÆŠalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

August 5, 2025
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

August 5, 2025
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

August 5, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

August 5, 2025
Tsauraran Manufofin Tattalin ArziÆ™in Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin ArziÆ™in Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.