• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayain da ake shirye-shiryen fara shukar alkama daga yanzu zuwa tsakiyar watan Dismba, manoman alkama a kasar nan, sun koka kan rashin samun iri.

A duk watan Dimsambar kowace shekara ce, manoman ke fara shirye-shiryen shukar alkamar, inda suka yi nuni da cewa, matsalar za ta iya shafar burin da suke da shi na samun amfani mai yawa, inda kuma hakan, zai kara janyo a samu wawagegen gibi na bukatar da ake da ita ta alkamar a kasar nan da ta kai fiye da tan miliayn 4.1.

  • Yadda Ake Cin Gajiyar ‘Google Drive’ Wajen Amfani Da Kwanfuta
  • Dalibin Da Ya Tsokani Aisha, Zai Gana Da Buhari A Villa

Wasu daga cikin maoman alkamar da aka tattauna da su a jihar Katsina sun bayyana cewa, duk da irin tsadar farashin takin zamani don yin noman na alkamar, sun nuna aniyarsu ta fara shukar alkamar a kan lokaci, domin su cike gibin da suka samu bara.

Daya daga cikin manoman na alkamar a jihar Katsaina Malam Murtala Mairuwa, ya koka kan rashin tallafin da manoman alkamar ba sa samu daga gwamnati, inda ya yi nuni da cewa, koda za su samu tallafin daga gun gwamnatin, ya an zuwa ne a makare

Sai dai, Mairuwa, ya ci gaba da cewa, kakar alkama a shekarar da ta wuce, gwamnatin ta samar wa da manoman dauki ta hanyar babban bankin Nijeriya CBN, musamman ta hanyar samar da takin zamani da sauran kayan aikin alkamar.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

A cewarsa, kamata ya yi a fara shuka Alkamar akalla daga cikin watan Nuwamba, inda hakan zai baiwa manomin ta damar samun yin girbin ta da dama, inda ya kara da cewa, ko a shekarar da ta wuce, an rabawar da manomanta da kayan aikin ne a cikin watan Disamba.

Mairuwa ya kara da cewa, wata matsalar da manoman ta ke fuskanta shine yadda ake samun wasu marsa kishi kuma wadanda suka kasance ba manonta ba, ke dakile zuwan daukin na gwamnatin ga ainahin manoman da ke yin nomanta.

Har ila yau, a cikin karamar hukumar Bakori da ke a cikin jihar Katsina, akasarin manomanta sun dogara ne akan samun ruwa daga kogin Jare domin yin noman ranin ta, inda daya daga cikin manoman nata Abdurrahman Kabir ya sanar da cewa, a kakar noman ta a wannan shekarra, ba a samu yawan ruwan sama da ake bukata ba

A cewar Kabir, manoman na alkamar a wannan shekarar, na fusntar kalubalen tsadar farashin kayan aikin na Alkamar, musamman idan aka yi la’akari da kudaden da suke kashewa wajen sayen man fetur domin yin ban ruwa.

An ce yanzu haka, farshin buhu day na alkamar mai nauyin kilo 100, ana sayar da shi kan naira 48,500 a kasuwar ta Bakori, inda kuma wasu sun ce, farshin ya kai sama da naira 50,000.

Har ila yau, a jihar Kano kuwa an ce, tuni wasu manoman alkamar suka fara koma wa gona domin fara yin aiki gadn-gadan, amma sai dai, abin takaici har yanzu ba su iya samun iri ba da kuma samun sauran dauki a fannin.

Biyo bayan wani bincike da aka gudanar sama da shekarun da suka wuce, alkasrin namoman na Alkamar sun fi dogara ne da samun Irin daga gun kafanonin da ke samar da irin domin sayawar da manoman.

A cewar wasu daga cikin manoman, tun lokacin da hukumar gudanar da bincike aikin noma da ke tabkin Chadi ta dakatar da raba da ingantaccen irin, an bar manoman da fafutukar nemo irin da ya dace.

Wani manominta a jihar Kano Alhaji Surajo Bello ya bayyana cewa, duk da karancin da ake fuskanta na alkamar a fadin duniya, a wannan shekarar, ba su samu daukin gwamnatin tarayya ta hanyar shirin noma na Anchor Borrower ba.

Ya ce, abin takaice ne ganin cewa duk da an sa manoman na Alkamar a cikin jeren manoman da za su amfana da daukin na babban bankin Nijeriya CBN, amma ba sa samun daukin.

Shi ma wani manoman na alkamar, Alhaji Musa Mu’azu Garun Babba ya sanar da cewa, shekaru da dama da suka wuce, an bar manoman na alkamar ne kawai suna sayen irin daga gun kamfanin da ke samar da irin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlkamaIriKokawaManomaNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Daga Karshe Dai Tawagar Su Dogara Sun Mara Wa Atiku Baya

Next Post

Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

Related

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

24 hours ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

1 day ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

2 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

1 week ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

1 week ago
Sin Ta Gina Cibiyoyin Fasahar Aikin Gona Na Gwaji Guda 24 A Afirka
Noma Da Kiwo

Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’

2 weeks ago
Next Post
Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

LABARAI MASU NASABA

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.