• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayain da ake shirye-shiryen fara shukar alkama daga yanzu zuwa tsakiyar watan Dismba, manoman alkama a kasar nan, sun koka kan rashin samun iri.

A duk watan Dimsambar kowace shekara ce, manoman ke fara shirye-shiryen shukar alkamar, inda suka yi nuni da cewa, matsalar za ta iya shafar burin da suke da shi na samun amfani mai yawa, inda kuma hakan, zai kara janyo a samu wawagegen gibi na bukatar da ake da ita ta alkamar a kasar nan da ta kai fiye da tan miliayn 4.1.

  • Yadda Ake Cin Gajiyar ‘Google Drive’ Wajen Amfani Da Kwanfuta
  • Dalibin Da Ya Tsokani Aisha, Zai Gana Da Buhari A Villa

Wasu daga cikin maoman alkamar da aka tattauna da su a jihar Katsina sun bayyana cewa, duk da irin tsadar farashin takin zamani don yin noman na alkamar, sun nuna aniyarsu ta fara shukar alkamar a kan lokaci, domin su cike gibin da suka samu bara.

Daya daga cikin manoman na alkamar a jihar Katsaina Malam Murtala Mairuwa, ya koka kan rashin tallafin da manoman alkamar ba sa samu daga gwamnati, inda ya yi nuni da cewa, koda za su samu tallafin daga gun gwamnatin, ya an zuwa ne a makare

Sai dai, Mairuwa, ya ci gaba da cewa, kakar alkama a shekarar da ta wuce, gwamnatin ta samar wa da manoman dauki ta hanyar babban bankin Nijeriya CBN, musamman ta hanyar samar da takin zamani da sauran kayan aikin alkamar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

A cewarsa, kamata ya yi a fara shuka Alkamar akalla daga cikin watan Nuwamba, inda hakan zai baiwa manomin ta damar samun yin girbin ta da dama, inda ya kara da cewa, ko a shekarar da ta wuce, an rabawar da manomanta da kayan aikin ne a cikin watan Disamba.

Mairuwa ya kara da cewa, wata matsalar da manoman ta ke fuskanta shine yadda ake samun wasu marsa kishi kuma wadanda suka kasance ba manonta ba, ke dakile zuwan daukin na gwamnatin ga ainahin manoman da ke yin nomanta.

Har ila yau, a cikin karamar hukumar Bakori da ke a cikin jihar Katsina, akasarin manomanta sun dogara ne akan samun ruwa daga kogin Jare domin yin noman ranin ta, inda daya daga cikin manoman nata Abdurrahman Kabir ya sanar da cewa, a kakar noman ta a wannan shekarra, ba a samu yawan ruwan sama da ake bukata ba

A cewar Kabir, manoman na alkamar a wannan shekarar, na fusntar kalubalen tsadar farashin kayan aikin na Alkamar, musamman idan aka yi la’akari da kudaden da suke kashewa wajen sayen man fetur domin yin ban ruwa.

An ce yanzu haka, farshin buhu day na alkamar mai nauyin kilo 100, ana sayar da shi kan naira 48,500 a kasuwar ta Bakori, inda kuma wasu sun ce, farshin ya kai sama da naira 50,000.

Har ila yau, a jihar Kano kuwa an ce, tuni wasu manoman alkamar suka fara koma wa gona domin fara yin aiki gadn-gadan, amma sai dai, abin takaici har yanzu ba su iya samun iri ba da kuma samun sauran dauki a fannin.

Biyo bayan wani bincike da aka gudanar sama da shekarun da suka wuce, alkasrin namoman na Alkamar sun fi dogara ne da samun Irin daga gun kafanonin da ke samar da irin domin sayawar da manoman.

A cewar wasu daga cikin manoman, tun lokacin da hukumar gudanar da bincike aikin noma da ke tabkin Chadi ta dakatar da raba da ingantaccen irin, an bar manoman da fafutukar nemo irin da ya dace.

Wani manominta a jihar Kano Alhaji Surajo Bello ya bayyana cewa, duk da karancin da ake fuskanta na alkamar a fadin duniya, a wannan shekarar, ba su samu daukin gwamnatin tarayya ta hanyar shirin noma na Anchor Borrower ba.

Ya ce, abin takaice ne ganin cewa duk da an sa manoman na Alkamar a cikin jeren manoman da za su amfana da daukin na babban bankin Nijeriya CBN, amma ba sa samun daukin.

Shi ma wani manoman na alkamar, Alhaji Musa Mu’azu Garun Babba ya sanar da cewa, shekaru da dama da suka wuce, an bar manoman na alkamar ne kawai suna sayen irin daga gun kamfanin da ke samar da irin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlkamaIriKokawaManomaNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Daga Karshe Dai Tawagar Su Dogara Sun Mara Wa Atiku Baya

Next Post

Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

2 days ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

2 days ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 week ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 week ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Next Post
Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.