• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayain da ake shirye-shiryen fara shukar alkama daga yanzu zuwa tsakiyar watan Dismba, manoman alkama a kasar nan, sun koka kan rashin samun iri.

A duk watan Dimsambar kowace shekara ce, manoman ke fara shirye-shiryen shukar alkamar, inda suka yi nuni da cewa, matsalar za ta iya shafar burin da suke da shi na samun amfani mai yawa, inda kuma hakan, zai kara janyo a samu wawagegen gibi na bukatar da ake da ita ta alkamar a kasar nan da ta kai fiye da tan miliayn 4.1.

  • Yadda Ake Cin Gajiyar ‘Google Drive’ Wajen Amfani Da Kwanfuta
  • Dalibin Da Ya Tsokani Aisha, Zai Gana Da Buhari A Villa

Wasu daga cikin maoman alkamar da aka tattauna da su a jihar Katsina sun bayyana cewa, duk da irin tsadar farashin takin zamani don yin noman na alkamar, sun nuna aniyarsu ta fara shukar alkamar a kan lokaci, domin su cike gibin da suka samu bara.

Daya daga cikin manoman na alkamar a jihar Katsaina Malam Murtala Mairuwa, ya koka kan rashin tallafin da manoman alkamar ba sa samu daga gwamnati, inda ya yi nuni da cewa, koda za su samu tallafin daga gun gwamnatin, ya an zuwa ne a makare

Sai dai, Mairuwa, ya ci gaba da cewa, kakar alkama a shekarar da ta wuce, gwamnatin ta samar wa da manoman dauki ta hanyar babban bankin Nijeriya CBN, musamman ta hanyar samar da takin zamani da sauran kayan aikin alkamar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

A cewarsa, kamata ya yi a fara shuka Alkamar akalla daga cikin watan Nuwamba, inda hakan zai baiwa manomin ta damar samun yin girbin ta da dama, inda ya kara da cewa, ko a shekarar da ta wuce, an rabawar da manomanta da kayan aikin ne a cikin watan Disamba.

Mairuwa ya kara da cewa, wata matsalar da manoman ta ke fuskanta shine yadda ake samun wasu marsa kishi kuma wadanda suka kasance ba manonta ba, ke dakile zuwan daukin na gwamnatin ga ainahin manoman da ke yin nomanta.

Har ila yau, a cikin karamar hukumar Bakori da ke a cikin jihar Katsina, akasarin manomanta sun dogara ne akan samun ruwa daga kogin Jare domin yin noman ranin ta, inda daya daga cikin manoman nata Abdurrahman Kabir ya sanar da cewa, a kakar noman ta a wannan shekarra, ba a samu yawan ruwan sama da ake bukata ba

A cewar Kabir, manoman na alkamar a wannan shekarar, na fusntar kalubalen tsadar farashin kayan aikin na Alkamar, musamman idan aka yi la’akari da kudaden da suke kashewa wajen sayen man fetur domin yin ban ruwa.

An ce yanzu haka, farshin buhu day na alkamar mai nauyin kilo 100, ana sayar da shi kan naira 48,500 a kasuwar ta Bakori, inda kuma wasu sun ce, farshin ya kai sama da naira 50,000.

Har ila yau, a jihar Kano kuwa an ce, tuni wasu manoman alkamar suka fara koma wa gona domin fara yin aiki gadn-gadan, amma sai dai, abin takaici har yanzu ba su iya samun iri ba da kuma samun sauran dauki a fannin.

Biyo bayan wani bincike da aka gudanar sama da shekarun da suka wuce, alkasrin namoman na Alkamar sun fi dogara ne da samun Irin daga gun kafanonin da ke samar da irin domin sayawar da manoman.

A cewar wasu daga cikin manoman, tun lokacin da hukumar gudanar da bincike aikin noma da ke tabkin Chadi ta dakatar da raba da ingantaccen irin, an bar manoman da fafutukar nemo irin da ya dace.

Wani manominta a jihar Kano Alhaji Surajo Bello ya bayyana cewa, duk da karancin da ake fuskanta na alkamar a fadin duniya, a wannan shekarar, ba su samu daukin gwamnatin tarayya ta hanyar shirin noma na Anchor Borrower ba.

Ya ce, abin takaice ne ganin cewa duk da an sa manoman na Alkamar a cikin jeren manoman da za su amfana da daukin na babban bankin Nijeriya CBN, amma ba sa samun daukin.

Shi ma wani manoman na alkamar, Alhaji Musa Mu’azu Garun Babba ya sanar da cewa, shekaru da dama da suka wuce, an bar manoman na alkamar ne kawai suna sayen irin daga gun kamfanin da ke samar da irin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlkamaIriKokawaManomaNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Daga Karshe Dai Tawagar Su Dogara Sun Mara Wa Atiku Baya

Next Post

Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

20 hours ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

21 hours ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

22 hours ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

1 week ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

1 week ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

2 weeks ago
Next Post
Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

LABARAI MASU NASABA

Yadda Za Ki Hada Funkasonki

Yadda Za Ki Hada Funkasonki

June 1, 2025
Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

May 31, 2025
CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

May 31, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

May 31, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

May 31, 2025
Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

May 31, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

May 31, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

May 31, 2025
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.